• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abun Da Aka Shuka Shi Za A Girba!

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Abun Da Aka Shuka Shi Za A Girba!
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani sakamakon bincike na jin raayin alumma, da jaridar The Guardian ta Amurka ta wallafa a baya bayan nan, ya nuna yadda duk cikin Amurkawa biyar, daya daga cikinsu ke ganin abu ne mai kyau, a cimma burin siyasa ta hanyar tarzoma.

Ko shakka babu hakan abun tsoro ne, da tayar da hankali, ganin cewa wannan tunani ya yi hannun riga da ainihin tushen dimokaradiyya, wanda ya tanadi cimma duk wani buri ta maslaha da kwanciyar hankali.

  • Sin Ta Mayar Da Martani Ga Rahoton Shekara-shekara Na Fataucin Bil Adama Na Amurka

Wani abun lura game da wannan bincike, shi ne yadda Amurkawa ke saurin yarda da farfagandar ’yan siyasa, wadda ke haifar da rashin yarda, da nuna kyama, da amincewa daukar matakan tada zaune tsaye, yayin da suke son cimma wani buri na siyasa ko zamantakewa.

Ko da yake dai Bahaushe kan ce Barewa ba za ta yi gudu dan ta ya yi rarrafe ba. Duniya ta ga misalin irin wannan tunani tun daga kan jagororin Amurka, inda alal misali, a ranar 6 ga watan Janairun shekarar bara, daruruwan magoya bayan tsohon shugaban kasar Donald Trump, suka yi kutse cikin ginin majalissar dokokin kasar na Capitol, da nufin hana bayyana tsohon shugaban kasar a matsayin wanda ya sha kaye a babban zaben da ya gabata.

Wanda hakan ya sabbaba rasuwar mutane 7 da jikkatar gwamman mutane. Masu bibiyar lamarin sun tabbatar da cewa shi kansa tsohon shugaba Trump, ya nuna wasu alamu na goyon bayan wancan kutse.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Masharhanta dai na ganin idan har wannan yanayi na yin watsi da tushen dimokaradiyya ya ci gaba da kamari a Amurka, mai yiwuwa kasar ta fuskanci manyan bore masu nasaba da siyasa a nan da ’yan shekaru masu zuwa.

Domin kaucewa hakan, wajibi ne jagororin kasar su yi karatun ta-nutsu, su yi hangen nesa wajen wayar da kan Amurkawa, game da illar dake tattare da daukar doka a hannu, da kin amincewa da mabanbantan raayoyi, da nuna isa, wadanda dukkaninsu munanan dabiu ne da ka iya haifarwa kasar da maras ido.

Uwa uba kuma, ya zama wajibi gwamnatin Amurka ta dawo daga rakiyar manufarta ta shiga sharo ba shanu, da nuna karfin tuwo ga sauran kasashe, ko nuna kyama ga hanyoyin ci gaba da sauran kasashe suka zabawa kan su, domin kuwa irin wannan tunani ne ke haifarwa ’yan kasar ta yanayi na kangarewa, da kin karbar gaskiya!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ba Za Ta Iya Bata Sunan Xinjiang Ba

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Zartar Da Dokar Hana Acaba

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

2 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

3 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

4 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

5 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

6 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

16 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Zartar Da Dokar Hana Acaba

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Zartar Da Dokar Hana Acaba

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.