• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 

by Sadiq
1 year ago
Malaman

Malaman addinin Musulunci a Jihar Kano sun yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya bai wa al’ummar jihar damar magance rikicin masarautar ba tare da amfani da karfin iko ba. 

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da jami’an tsaro ke ci gaba da kokarin samar da zaman lafiya a jihar.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gina Gidaje Masu Saukin Kudi 1,250 A Jihohi Hudu
  • Jami’an Tsaro Na Ganawar Sirri Da Abba Da Sarki Sanusi II A Fadar Kano

Malaman sun bayyana matukar damuwarsu dangane da tashe-tashen hankulan da ke faruwa a masarautar, inda suka bukaci Gwamnatin Tarayya da ta sa baki domin wanzuwar zaman lafiya.

A cikin wata sanarwa da Shaikh Abdullahi Uwais Limanci ya sanya wa hannu, malaman sun yi gargadin cewa lamarin na iya haifar da tashin-tashina.

Sanarwar ta kara da cewa “Jihar Kano na daya daga cikin jihohin da aka fi samun zaman lafiya a Nijeriya duk da sarkakiyar siyasarta, ya zama wajibi shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dauki dukkan matakan da suka dace domin wanzar da zaman lafiya a jihar.”

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Malaman sun jaddada muhimmancin barin al’ummar Kano wajen warware matsalolinsu cikin ruwan sanyi, ba tare da yin amfani da karfi ba wanda a cewarsu hakan zai iya haifar da asarar rayuka.

Sun bayyana muhimmancin tattaunawa da mutunta juna wajen tunkarar rikicin da ke faruwa a yanzu.

“Muna kira ga mai girma shugaban kasa da ya bai wa al’ummar Jihar Kano damar magance wadannan matsaloli cikin ruwan sanyi ba tare da yin amfani da karfi da zai kai ga asarar rayuka da dukiyoyi ba.

Gammayar kungiyar malaman ta kuma yi kira ga bangarorin sarakunan da ke rikici da juna da su yi amfani da hanyoyi da suka dace don sim zaman lafiya a tsakaninsu.

Malaman sun yi alkawarin shiga tsakani tare da tuntubar duk bangarorin da abin ya shafa don samar da mafita cikin lumana.

A halin yanzu dai al’amura sun fara daidaita a jihar, bayan da shugaban hukumomin tsaro a jihar suka gana da duka bangarorin biyu da suka hada da tsagin sabon Sarki Sanusi Lamido II wanda ke samun goyon bayan gwamnati mai ci.

Sai kuma tsagin tsohon Sarki Aminu Ado Bayero, wanda wasu rahotanni suka bayyana yana samun goyon baya daga sama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
Manyan Labarai

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Next Post
Bankin TAJBank Ya Sake Lashe Kambun Gwarzon Bankin Musulunci A Nijeriya

Bankin TAJBank Ya Sake Lashe Kambun Gwarzon Bankin Musulunci A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.