• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Kafa Tarihi A Gasar Firimiyar Ingila Da Aka Kammala

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Tarihi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kammala gasar Premier League ranar Lahadi 19 ga watan Mayu da wasa 10 a filaye daban daban a kuma lokaci daya wanda hakan ne ya kawo karshen wasannin kakar wasa ta 2023 zuwa 2024. Wannan ita ce daya daga babbar gasar kwallon kafa ta Ingila da ba a taba yin irinta ba a tarihi – ga jerin wasu abubuwan tarihin da aka yi.

Cin kwallaye:
Kenan an zura kwallaye 1,246 a kakar da aka kammala, sai dai a kakar wasa ta 1992 zuwa 1993 wadda aka yi wasanni 462, an ci kwallo 1,222, kenan duk da haka an fi zura kwallaye a wannan kakar idan aka kwatanta da ta shekarar.

Dan wasan Manchester City, Erling Haaland shi ne kan gaba a cin kwallaye a bana, wanda yake da 27 a raga kuma a bara shi ne ya lashe takalmin zinare a matakin wanda ya zura kwallaye da yawa a raga mai 36 jimilla.

Ga kuma Jerin wadanda suka fi zura kwallaye a raga:
Erling Haaland Manchester City 27. Sai Cole Palmer 20 Chelsea 22, sannan Aledander Isak Newcastle United 21. Ollie Watkins Aston Billa 19. Dominic Solanke Bournemouth 19. Mohamed Salah Liberpool 18. Heung-min Son Tottenham 17. Phil Foden manchester City 19. Bukayo Saka Arsenal 16. Jarrod Bowen West Ham United 16.

Wadanda ke kan gaba a cin kwallo a kakar wasa ta 2022 zuwa 2023.
Erling Haaland Manchester City 36, sannan Harry Kane Tottenham 30. Iban Toney Brentford 20. Mohamed Salah Liberpool 19. Callum Wilson Newcastle United 18
Marcus Rashford Manchester United 17. Martin Odegaard Arsenal 15. Ollie Watkins Aston Billa 15. Gabriel Martinelli Arsenal 15. Semenyo, Bournemouth.

Labarai Masu Nasaba

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Cin kwallaye na kayatar da wasan kwallo, kuma a kakar nan an ci wasa a karawar da ake tsammani kungiya za ta yi rashin nasara, amma daga baya ta lashe fafatawar, inda aka yi haka har sau 62.

Karon farko da aka samu wannan kwazon tun da aka fara gasar Premier League a tarihin wasannin daga 2008 zuwa 2009, sannan an kuma farke kwallo a wasa sau 223, karo na biyu a wannan kwazon a gasar ta Premier League tun bayan 237 da aka yi a 1993 zuwa 1994.

Raba kwallo tsakanin ‘yan wasa kan taimaka wa kungiya wajen mamaye gasa, yana kuma nuna kwazo da kwarewar ‘yan kwallo da kociyan dake jan ragamar wannan kungiya.
An bayar da kwallo zuwa abokin wasa kamar yadda ya kamata kaso 83 cikin 100, wato passing, wannan ita ce bajinta ta farko daga kakar wasa 16 tun daga kakar wasa ta 2008 zuwa 2009.

Aston Billa ta zama kungiya ta takwas daga Premier League a kaka uku baya da ta samu gurbin Champions League, ba cikin wadanda suka saba zuwa wasannin gasar ba.

Yadda aka yi neman lashe Premier League
A karo na uku kenan a jere ake fayyace wadda za ta lashe Premier League a ranar karshen gasar, kuma karo na 10 a tarihi kuma makin da yake raba kungiya ta daya da ta biyu baya wuce 1.51, sai dai tun daga 1992/93 ba a samu tazarar maki mafi karanci ba tsakayin ta daya da ta biyun teburin ba. Kungiyoyi bakwai ne suka ja ragamar teburin Premier League a kakar nan.
Kwanakin da kungiya ta yi a saman teburin Premier a kakar wasa ta 2023 zuwa 2024 Liberpool kwana 87, Arsenal kwana 76, Man City kwana 76, Tottenham kwana 26, Brighton kwana 7, Newcastle kwana 7, West Ham kwana 2, An samu matasa da yawa da suka fara buga Premier League a bana.
‘Yan wasan waje ke bayar da gudunmuwa da yawa a gasar Premier League, sai dai wannan karon a samu matasa 61 da suka fara yin kakar bana da su, karo na uku da aka samu da yawa kenan.

Haka kuma ‘yan wasan Ingila sun ci kwallo 359 a bana a gasar da suka zura kwallaye da yawa tun bayan kakar wasa ta 2001 zuwa 2002 – inda ‘yan wasan Ingila shida ke cikin goman farko a yawan cin kwallaye a gasar.

Cole Palmer
‘‘Yan wasa 68 daga kasashen duniya daban-daban ne suka buga Premier League a kakar nan, wadanda ake fara wasa da su a cikin fili tsakanin kungiyoyi 20 da suka kara a bana.
Tun daga sauya fasalin gasar ta Premier League daga shekarar 1992 zuwa 1993, an samu ‘yan wasa 123 daga kasashen duniya da suka buga babbar gasar.

Matsakaicin shekarar ‘yan wasa a kakar nan ya fara daga 26 da kwana 169 kan fara – mafi karancin shekara tun daga kakar wasa ta 2008 zuwa 2009 kuma karo na hudu a karancin shekara a gasar.

’Yan kallo da yawa a filayen wasanni.
Filayen wasa kan dauki ‘yan kallo kaso 98.7 cikin 100 a Premier League ta kakar nan, wadda ta yi kan-kan-kan da tarihin kakar bara kuma daga cikin kungiyoyi 20 da suke buga gasar kakar nan, guda 18 kan samu ‘yan kallo kaso 97 cikin 100. Wasan Liberpool da Tottenham – Premier League. Akwai wasa 10 da aka kalli kai tsaye a talabijin da mutum miliyan uku kowanne suka gani a Burtaniya a kakar nan, kakar da aka fi kallo wadda ta haura ta ita ce kakar wasa ta 2019 zuwa 2020.

Jimilla mutum miliyan 37.7 suka kalli wasa kai tsaye a talabijin da kuma sharhin kwallo na BBC Match of the Day, kimanin kaso 59 cikin 100 a Burtaniya kamar yadda alkaluma suka nuna.

Yadda duniya ke bibiyar Premier League.
Gasar Premier League ta zama mafi girma mai dan karen farin jini a wasan da ake bibiya a Burtaniya da kuma fadin duniya kuma an nuna gasar tsakanin kasashe 189 daga mambobin majalissar dinkin duniya 193 tsakanin gida miliyan 900.

Mutum biliyan 1.87 suke bibiyar Premier League a fadin duniya, wadanda ke tafka muhawara a duk mako a kafar sada zumunta da ta sadarwa, sannan an samu kaso 34 cikin 100 da suke bibiyar Premier League sau da kafa a kaka ta hudu a jere kenan.

Mutane da yawa sun kalli wasa Arsenal da City a Nashville
Wasan Manchester City da Arsenal da aka buga a Premier League ranar 31 ga watan Maris ya zama kan gaba da aka fi kallo a tarihin Amurka, inda mutum miliyan 2.12 da suka kalla a kafar sadarwa ta NBC.
Wasu karin kididigar Premier League
An fara kakar bana daga 11 ga watan Agustan 2023.

Wadanda suka fadi daga kakar bana
Burnley, Sheffield United, Luton Town,
Gurbin Champions League
Manchester City, Arsenal, Liberpool, Aston Billa,
Wasannin da aka buga: 370. Kwallayen da aka ci kawo yanzu: 1,246.
Wanda yake kan gaba a cin kwallaye: Erling Haaland Man City 27 a raga. Fitatcen mai tsaron raga: Dabid Raya (Wasa 16 kwallo bata shiga raga ba)
Wasan da aka ci kwallo da yawa a gida: Chelsea 6–0 Eberton (15
Afirilun 2024)
Wanda aka ci kwallo da yawa a waje: Sheffield United 0–8 Newcastle
United (24 ga watan Satumbar 2023)
Wasannin da aka ci kwallaye da yawa a raga: Sheffield United 0–8 Newcastle United (24 ga watan Satumbar 2023) Chelsea 4–4 Manchester City (12 ga watan Nuwambar 2023). Newcastle United 4–4 Luton Town (3 ga watan Fabrairun 2024). Yawan cin wasa 8 a jere: Arsenal da Manchester City.
Wasa 22 ba tare da rashin nasara ba a jere: Manchester City Wasa 13 ba tare da nasara ba: Eberton da Sheffield United. Wasa shida a jere da rashin nasara: Burnley da Sheffield United. Wasan da ya dauki ‘yan kallo 73,612 Manchester United 3–0 West Ham United (4 ga watan Fabrairu 2024)
Wasan da bai yi mutane ba a filin wasa 10,421
Bournemouth 0–0 Chelsea (17 ga wwatan Satatumba 2023)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalLiverpoolManchester CityMarseille
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin Tazarar Haihuwa Mara Amfani Da Magani (1)

Next Post

An Bayar Da Belin DCP Abba Kyari

Related

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

1 day ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

3 days ago
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

5 days ago
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa
Wasanni

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

5 days ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

6 days ago
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica
Wasanni

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

6 days ago
Next Post
An Bayar Da Belin DCP Abba Kyari

An Bayar Da Belin DCP Abba Kyari

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.