ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

by Abba Ibrahim Wada
10 months ago
Nijeriya

An rufe kasuwar musayar yan kwallo ta shekarar 2025 a manyan gasannin kwallon kafa 5 dake Turai, (Premier League, Serie A, LaLiga, Bundesliga da Ligue 1) a daren Litinin.

LEADERSHIP Hausa ta zakulo maku yadda ta kaya da wasu ‘yan wasan Nijeriya a kasuwar musamman a ranar da aka rufe, wasu sun canza kungiyoyi walau a matsayin dindindin ko a matsayin aro, yayin da wasu kuma suka ci gaba da zama tare da kungiyoyinsu na yanzu bayan sun rasa damar komawa wasu kungiyoyi kafin a rufe kasuwar musayar yan wasa a daren Litinin.

Samuel Chukwueze

ADVERTISEMENT

Samuel Chukwueze ya bar Ac Milan zuwa kungiyar Fulham dake buga gasar Firimiya a ranar Litinin, dan wasan wanda aka bai wa riga mai lamba 19 a Fulham, ya bar kungiyar AC Milan ta Seria A domin ya kammala saka hannu a yarjejeniyar zaman aro na tsawon kakar wasa guda sukutum a Fulham din, dan wasan mai shekaru 26 zai iske abokan wasansa a Nijeriya Aled Iwobi da Calbin Bassey.

 

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Bictor Boniface

Wani dan wasan da ya tafi zaman aro shi ne Bictor Boniface wanda ya bar Bayer Leberkusen ya koma Werder Bremen a matsayin aro na tsawon kaka guda a ranar da za a rufe cinikin yan wasa, dan wasan na Nijeriya ya saka hannu akan kwantiragin da zai sa ya zauna a Werder har zuwa watan Yuni na shekarar 2026, kungiyoyin biyu ne za su biya albashin Boniface.

 

Tolu Arokodare

Wolbes ta sanar da daukar Arokodare daga kungiyar KRC Genk ta kasar Belgium dake buga gasar Belgian Pro League a ranar karshe ta musayar yan wasa, dan wasan mai shekaru 24 ya rattaba hannu kan kwantiragin shekaru hudu da kungiyar ta Firimiya tare da zabin karin shekara, Arokodare ya koma Wolbes ne bayan ya buga wasa mai ban shaawa a kungiyar Genk a kakar wasan da ta wuce, inda ya kare a matsayin dan wasan da ya fi zura kwallaye a gasar ta Belgium da kwallaye 21.

 

Wilfred Ndidi

Ndidi ya koma kungiyar Besiktas dake buga gasar Super Lig ta kasar Turkiyya daga Leicester City a farkon kasuwar musayar yan wasa, dan wasan na Nijeriya ya koma kungiyar ta Turkiyya ne kan kwantiragin shekaru uku a watan Agusta, an danganta dan wasan mai shekaru 28 da kungiyoyi da dama a Turai amma ya zabi komawa Besiktas.

 

Bictor Osimhen

Osimhen ya koma Galatasaray ne kan kwantiragin shekaru hudu daga Napoli a farkon wannan bazarar bayan da zakarun Super Lig na Turkiyya suka yanke shawarar biyan Yuro miliyan 75 domin daukarshi, Osimhen, wanda zai samu albashin Yuro miliyan 15 a duk shekara, tuni ya ci wa Galatasaray kwallaye biyu a kakar wasa ta bana, dan wasan na Nijeriya ya ci wa Galatasaray kwallaye 37 a dukkan wasannin da ya buga a bara.

 

Chidozie Awaziem

Mai tsaron bayan ya dawo Faransa daga MLS, inda ya bar Colorado Rapids ya koma Nantes kan kwantiragin shekaru uku.

 

Moses Simon

Simon ya kammala komawa kulob din Faransa dake buga gasar Ligue 1, Paris FC a farkon wannan bazara, dan wasan mai shekaru 29, ya koma Paris FC ne daga Nantes kan kwantiragin shekaru uku, kan kudi Yuro miliyan 7, dan wasan ya ci kwallaye takwas sannan ya taimaka wajen cin 10 a wasanni 32 da ya buga wa Nantes a bara.

 

Gift Orban

Dan wasan mai shekaru 22 ya bar Lyon zuwa Hoffenheim a kan Yuro miliyan 9 tare da karin kudi na Yuro miliyan 3, tuni dai ya bude asusunsa a kasar Jamus inda ya zura kwallo a raga a wasansa na farko da kungiyar inda aka tashi 2-2.

Dukkan wadannan yan wasa dake buga kwallo a kasashen Turai na daga cikin wadanda kocin tawagar Super Eagles ta Nijeriya Eric Chelle zai iya gayyata domin wakiltar Nijeriya a wasannin neman tikitin buga gasar Kofin Duniya da za a cigaba da bugawa a wannan watan na Satumba da ya kama, Osimhen, Moses Simon da Samuel Chukwuze na daga cikin yan wasan gaba da Nijeriya ke ji dasu a cikin tawagarta, hakazalika a lokuta da dama yan wasan sun sha fitar wa kasar kitse a wuta a wasanni masu muhimmanci.

Yayin da wasannin neman tikitin shiga gasar cin kofin Duniya na FIFA ke gabatowa mako mai zuwa, yana da muhimmanci wadannan yan wasan su kasance cikin natsuwa domin wakiltar Nijeriya a wadannan wasannin, tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta kara da takwarorinta na kasar Rwanda da Afirka ta Kudu a wannan watan.

 

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.