ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
Nijeriya

An rufe kasuwar musayar yan kwallo ta shekarar 2025 a manyan gasannin kwallon kafa 5 dake Turai, (Premier League, Serie A, LaLiga, Bundesliga da Ligue 1) a daren Litinin.

LEADERSHIP Hausa ta zakulo maku yadda ta kaya da wasu ‘yan wasan Nijeriya a kasuwar musamman a ranar da aka rufe, wasu sun canza kungiyoyi walau a matsayin dindindin ko a matsayin aro, yayin da wasu kuma suka ci gaba da zama tare da kungiyoyinsu na yanzu bayan sun rasa damar komawa wasu kungiyoyi kafin a rufe kasuwar musayar yan wasa a daren Litinin.

Samuel Chukwueze

ADVERTISEMENT

Samuel Chukwueze ya bar Ac Milan zuwa kungiyar Fulham dake buga gasar Firimiya a ranar Litinin, dan wasan wanda aka bai wa riga mai lamba 19 a Fulham, ya bar kungiyar AC Milan ta Seria A domin ya kammala saka hannu a yarjejeniyar zaman aro na tsawon kakar wasa guda sukutum a Fulham din, dan wasan mai shekaru 26 zai iske abokan wasansa a Nijeriya Aled Iwobi da Calbin Bassey.

 

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Bictor Boniface

Wani dan wasan da ya tafi zaman aro shi ne Bictor Boniface wanda ya bar Bayer Leberkusen ya koma Werder Bremen a matsayin aro na tsawon kaka guda a ranar da za a rufe cinikin yan wasa, dan wasan na Nijeriya ya saka hannu akan kwantiragin da zai sa ya zauna a Werder har zuwa watan Yuni na shekarar 2026, kungiyoyin biyu ne za su biya albashin Boniface.

 

Tolu Arokodare

Wolbes ta sanar da daukar Arokodare daga kungiyar KRC Genk ta kasar Belgium dake buga gasar Belgian Pro League a ranar karshe ta musayar yan wasa, dan wasan mai shekaru 24 ya rattaba hannu kan kwantiragin shekaru hudu da kungiyar ta Firimiya tare da zabin karin shekara, Arokodare ya koma Wolbes ne bayan ya buga wasa mai ban shaawa a kungiyar Genk a kakar wasan da ta wuce, inda ya kare a matsayin dan wasan da ya fi zura kwallaye a gasar ta Belgium da kwallaye 21.

 

Wilfred Ndidi

Ndidi ya koma kungiyar Besiktas dake buga gasar Super Lig ta kasar Turkiyya daga Leicester City a farkon kasuwar musayar yan wasa, dan wasan na Nijeriya ya koma kungiyar ta Turkiyya ne kan kwantiragin shekaru uku a watan Agusta, an danganta dan wasan mai shekaru 28 da kungiyoyi da dama a Turai amma ya zabi komawa Besiktas.

 

Bictor Osimhen

Osimhen ya koma Galatasaray ne kan kwantiragin shekaru hudu daga Napoli a farkon wannan bazarar bayan da zakarun Super Lig na Turkiyya suka yanke shawarar biyan Yuro miliyan 75 domin daukarshi, Osimhen, wanda zai samu albashin Yuro miliyan 15 a duk shekara, tuni ya ci wa Galatasaray kwallaye biyu a kakar wasa ta bana, dan wasan na Nijeriya ya ci wa Galatasaray kwallaye 37 a dukkan wasannin da ya buga a bara.

 

Chidozie Awaziem

Mai tsaron bayan ya dawo Faransa daga MLS, inda ya bar Colorado Rapids ya koma Nantes kan kwantiragin shekaru uku.

 

Moses Simon

Simon ya kammala komawa kulob din Faransa dake buga gasar Ligue 1, Paris FC a farkon wannan bazara, dan wasan mai shekaru 29, ya koma Paris FC ne daga Nantes kan kwantiragin shekaru uku, kan kudi Yuro miliyan 7, dan wasan ya ci kwallaye takwas sannan ya taimaka wajen cin 10 a wasanni 32 da ya buga wa Nantes a bara.

 

Gift Orban

Dan wasan mai shekaru 22 ya bar Lyon zuwa Hoffenheim a kan Yuro miliyan 9 tare da karin kudi na Yuro miliyan 3, tuni dai ya bude asusunsa a kasar Jamus inda ya zura kwallo a raga a wasansa na farko da kungiyar inda aka tashi 2-2.

Dukkan wadannan yan wasa dake buga kwallo a kasashen Turai na daga cikin wadanda kocin tawagar Super Eagles ta Nijeriya Eric Chelle zai iya gayyata domin wakiltar Nijeriya a wasannin neman tikitin buga gasar Kofin Duniya da za a cigaba da bugawa a wannan watan na Satumba da ya kama, Osimhen, Moses Simon da Samuel Chukwuze na daga cikin yan wasan gaba da Nijeriya ke ji dasu a cikin tawagarta, hakazalika a lokuta da dama yan wasan sun sha fitar wa kasar kitse a wuta a wasanni masu muhimmanci.

Yayin da wasannin neman tikitin shiga gasar cin kofin Duniya na FIFA ke gabatowa mako mai zuwa, yana da muhimmanci wadannan yan wasan su kasance cikin natsuwa domin wakiltar Nijeriya a wadannan wasannin, tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta kara da takwarorinta na kasar Rwanda da Afirka ta Kudu a wannan watan.

 

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.