ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
Nijeriya

An rufe kasuwar musayar yan kwallo ta shekarar 2025 a manyan gasannin kwallon kafa 5 dake Turai, (Premier League, Serie A, LaLiga, Bundesliga da Ligue 1) a daren Litinin.

LEADERSHIP Hausa ta zakulo maku yadda ta kaya da wasu ‘yan wasan Nijeriya a kasuwar musamman a ranar da aka rufe, wasu sun canza kungiyoyi walau a matsayin dindindin ko a matsayin aro, yayin da wasu kuma suka ci gaba da zama tare da kungiyoyinsu na yanzu bayan sun rasa damar komawa wasu kungiyoyi kafin a rufe kasuwar musayar yan wasa a daren Litinin.

Samuel Chukwueze

ADVERTISEMENT

Samuel Chukwueze ya bar Ac Milan zuwa kungiyar Fulham dake buga gasar Firimiya a ranar Litinin, dan wasan wanda aka bai wa riga mai lamba 19 a Fulham, ya bar kungiyar AC Milan ta Seria A domin ya kammala saka hannu a yarjejeniyar zaman aro na tsawon kakar wasa guda sukutum a Fulham din, dan wasan mai shekaru 26 zai iske abokan wasansa a Nijeriya Aled Iwobi da Calbin Bassey.

 

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Bictor Boniface

Wani dan wasan da ya tafi zaman aro shi ne Bictor Boniface wanda ya bar Bayer Leberkusen ya koma Werder Bremen a matsayin aro na tsawon kaka guda a ranar da za a rufe cinikin yan wasa, dan wasan na Nijeriya ya saka hannu akan kwantiragin da zai sa ya zauna a Werder har zuwa watan Yuni na shekarar 2026, kungiyoyin biyu ne za su biya albashin Boniface.

 

Tolu Arokodare

Wolbes ta sanar da daukar Arokodare daga kungiyar KRC Genk ta kasar Belgium dake buga gasar Belgian Pro League a ranar karshe ta musayar yan wasa, dan wasan mai shekaru 24 ya rattaba hannu kan kwantiragin shekaru hudu da kungiyar ta Firimiya tare da zabin karin shekara, Arokodare ya koma Wolbes ne bayan ya buga wasa mai ban shaawa a kungiyar Genk a kakar wasan da ta wuce, inda ya kare a matsayin dan wasan da ya fi zura kwallaye a gasar ta Belgium da kwallaye 21.

 

Wilfred Ndidi

Ndidi ya koma kungiyar Besiktas dake buga gasar Super Lig ta kasar Turkiyya daga Leicester City a farkon kasuwar musayar yan wasa, dan wasan na Nijeriya ya koma kungiyar ta Turkiyya ne kan kwantiragin shekaru uku a watan Agusta, an danganta dan wasan mai shekaru 28 da kungiyoyi da dama a Turai amma ya zabi komawa Besiktas.

 

Bictor Osimhen

Osimhen ya koma Galatasaray ne kan kwantiragin shekaru hudu daga Napoli a farkon wannan bazarar bayan da zakarun Super Lig na Turkiyya suka yanke shawarar biyan Yuro miliyan 75 domin daukarshi, Osimhen, wanda zai samu albashin Yuro miliyan 15 a duk shekara, tuni ya ci wa Galatasaray kwallaye biyu a kakar wasa ta bana, dan wasan na Nijeriya ya ci wa Galatasaray kwallaye 37 a dukkan wasannin da ya buga a bara.

 

Chidozie Awaziem

Mai tsaron bayan ya dawo Faransa daga MLS, inda ya bar Colorado Rapids ya koma Nantes kan kwantiragin shekaru uku.

 

Moses Simon

Simon ya kammala komawa kulob din Faransa dake buga gasar Ligue 1, Paris FC a farkon wannan bazara, dan wasan mai shekaru 29, ya koma Paris FC ne daga Nantes kan kwantiragin shekaru uku, kan kudi Yuro miliyan 7, dan wasan ya ci kwallaye takwas sannan ya taimaka wajen cin 10 a wasanni 32 da ya buga wa Nantes a bara.

 

Gift Orban

Dan wasan mai shekaru 22 ya bar Lyon zuwa Hoffenheim a kan Yuro miliyan 9 tare da karin kudi na Yuro miliyan 3, tuni dai ya bude asusunsa a kasar Jamus inda ya zura kwallo a raga a wasansa na farko da kungiyar inda aka tashi 2-2.

Dukkan wadannan yan wasa dake buga kwallo a kasashen Turai na daga cikin wadanda kocin tawagar Super Eagles ta Nijeriya Eric Chelle zai iya gayyata domin wakiltar Nijeriya a wasannin neman tikitin buga gasar Kofin Duniya da za a cigaba da bugawa a wannan watan na Satumba da ya kama, Osimhen, Moses Simon da Samuel Chukwuze na daga cikin yan wasan gaba da Nijeriya ke ji dasu a cikin tawagarta, hakazalika a lokuta da dama yan wasan sun sha fitar wa kasar kitse a wuta a wasanni masu muhimmanci.

Yayin da wasannin neman tikitin shiga gasar cin kofin Duniya na FIFA ke gabatowa mako mai zuwa, yana da muhimmanci wadannan yan wasan su kasance cikin natsuwa domin wakiltar Nijeriya a wadannan wasannin, tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta kara da takwarorinta na kasar Rwanda da Afirka ta Kudu a wannan watan.

 

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.