• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar ‘Yan Ƙwadago Kan Mafi Ƙarancin Albashi ₦494,000 Duk Shekara Zai Kai Naira Tiriliyan 9.5 Kuma Ba Zai Dore Ba – Minista

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Yajin aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya ce mafi ƙarancin albashi na ƙasa N494,000 da Ƙungiyar Ƙwadago (NLC) ke nema, wanda ya kai jimillar naira tiriliyan 9.5 a duk shekara, na iya gurgunta tattalin arzikin ƙasa da kuma kawo cikas ga jin daɗin ‘yan Nijeriya sama da miliyan 200.

Idris ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai a Abuja, yayin da yake mayar da martani ga barazanar da ƙungiyar ƙwadagon ta yi na tafiya yajin aiki idan har ba a biya musu buƙatunsu ba.

  • Wakilin Sin: Kasar Sin Ta Goyi Bayan Falasdinu Wajen Taka Rawar Gani A WHO 
  • Gwamna Dauda Ya Biya Bashin Giratuti Na Shekara 13 Da Aka Riƙe Wa Ma’aikatan Zamfara

Ya ce tayin na N60,000 da Gwamnatin Tarayya ta yi, wanda ya kai ƙarin kashi 100 na mafi ƙarancin albashin da ake biya na shekarar 2019, ya samu karɓuwa daga ƙungiyar masu zaman kansu, wacce mamba ce na kwamitin ɓangarori uku na tattaunawar.

“Sabon tsarin albashi mafi ƙaranci na Gwamnatin Tarayya ya kai kashi 100 a kan mafi ƙarancin albashin da ake biya na shekarar 2019. Amma Ƙungiyar Ƙwadago ta buƙaci N494,000, wanda zai ƙaru da kashi 1,547 a kan albashin da ake biya.

“Mafi ƙarancin albashi N494,000 na ƙasa da ma’aikata ke nema zai kai adadin naira tiriliyan 9.5 da Gwamnatin Tarayya za ta biya.

Labarai Masu Nasaba

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

“Ya kamata ‘yan Nijeriya su fahimci cewa, duk da cewa Gwamnatin Tarayya na son a ba ma’aikatan Nijeriya isasshen albashi, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ba zai ƙarfafa duk wani mataki da zai kai ga asara mai ɗimbin yawa na ayyuka ba, musamman a kamfanoni masu zaman kansu, waɗanda ba za su iya biyan albashin da Ƙungiyar Ƙwadago ta nema ba,” inji shi.

Ministan ya ce duk da cewa Ƙungiyar Ƙwadago ta damu da albashin ma’aikata kusan miliyan 1.2, Gwamnatin Tarayya ta damu da jin daɗin ‘yan Nijeriya sama da miliyan 200 bisa la’akari da ƙa’idojinta na araha, ɗorewa, da kuma lafiyar tattalin arzikin ƙasar baki ɗaya.

Idris ya yi kira ga Ƙungiyar Ƙwadago da ta koma kan teburin tattaunawa tare da rungumar albashi mai ma’ana da gaskiya ga mambobinsu.

Ya ce saboda jajircewar da gwamnatin Tinubu ta yi wajen kyautata rayuwar ma’aikata, za a ci gaba da bayar da albashin ma’aikatan tarayya N35,000 har sai an ɓullo da sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NlcTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Dauda Ya Biya Bashin Giratuti Na Shekara 13 Da Aka Riƙe Wa Ma’aikatan Zamfara

Next Post

Gobe Za a Tsunduma Yajin Aiki, An Gaza Cimma matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC

Related

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

7 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

8 hours ago
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

9 hours ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

11 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

13 hours ago
Next Post
Gobe Za a Tsunduma Yajin Aiki, An Gaza Cimma matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC

Gobe Za a Tsunduma Yajin Aiki, An Gaza Cimma matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.