ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar ‘Yan Ƙwadago Kan Mafi Ƙarancin Albashi ₦494,000 Duk Shekara Zai Kai Naira Tiriliyan 9.5 Kuma Ba Zai Dore Ba – Minista

by Sulaiman
2 years ago
Yajin aiki

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya ce mafi ƙarancin albashi na ƙasa N494,000 da Ƙungiyar Ƙwadago (NLC) ke nema, wanda ya kai jimillar naira tiriliyan 9.5 a duk shekara, na iya gurgunta tattalin arzikin ƙasa da kuma kawo cikas ga jin daɗin ‘yan Nijeriya sama da miliyan 200.

Idris ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai a Abuja, yayin da yake mayar da martani ga barazanar da ƙungiyar ƙwadagon ta yi na tafiya yajin aiki idan har ba a biya musu buƙatunsu ba.

  • Wakilin Sin: Kasar Sin Ta Goyi Bayan Falasdinu Wajen Taka Rawar Gani A WHO 
  • Gwamna Dauda Ya Biya Bashin Giratuti Na Shekara 13 Da Aka Riƙe Wa Ma’aikatan Zamfara

Ya ce tayin na N60,000 da Gwamnatin Tarayya ta yi, wanda ya kai ƙarin kashi 100 na mafi ƙarancin albashin da ake biya na shekarar 2019, ya samu karɓuwa daga ƙungiyar masu zaman kansu, wacce mamba ce na kwamitin ɓangarori uku na tattaunawar.

ADVERTISEMENT

“Sabon tsarin albashi mafi ƙaranci na Gwamnatin Tarayya ya kai kashi 100 a kan mafi ƙarancin albashin da ake biya na shekarar 2019. Amma Ƙungiyar Ƙwadago ta buƙaci N494,000, wanda zai ƙaru da kashi 1,547 a kan albashin da ake biya.

“Mafi ƙarancin albashi N494,000 na ƙasa da ma’aikata ke nema zai kai adadin naira tiriliyan 9.5 da Gwamnatin Tarayya za ta biya.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

“Ya kamata ‘yan Nijeriya su fahimci cewa, duk da cewa Gwamnatin Tarayya na son a ba ma’aikatan Nijeriya isasshen albashi, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ba zai ƙarfafa duk wani mataki da zai kai ga asara mai ɗimbin yawa na ayyuka ba, musamman a kamfanoni masu zaman kansu, waɗanda ba za su iya biyan albashin da Ƙungiyar Ƙwadago ta nema ba,” inji shi.

Ministan ya ce duk da cewa Ƙungiyar Ƙwadago ta damu da albashin ma’aikata kusan miliyan 1.2, Gwamnatin Tarayya ta damu da jin daɗin ‘yan Nijeriya sama da miliyan 200 bisa la’akari da ƙa’idojinta na araha, ɗorewa, da kuma lafiyar tattalin arzikin ƙasar baki ɗaya.

Idris ya yi kira ga Ƙungiyar Ƙwadago da ta koma kan teburin tattaunawa tare da rungumar albashi mai ma’ana da gaskiya ga mambobinsu.

Ya ce saboda jajircewar da gwamnatin Tinubu ta yi wajen kyautata rayuwar ma’aikata, za a ci gaba da bayar da albashin ma’aikatan tarayya N35,000 har sai an ɓullo da sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa.

Kwadago
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Gobe Za a Tsunduma Yajin Aiki, An Gaza Cimma matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC

Gobe Za a Tsunduma Yajin Aiki, An Gaza Cimma matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.