• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Wajaba EU Ta Dawo Daga Rakiyar Matakan Gurgunta Tsarin Cinikayya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Wajaba EU Ta Dawo Daga Rakiyar Matakan Gurgunta Tsarin Cinikayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da kiraye-kiraye da kasar Sin ta rika yi don gane da bukatar warware takaddamar cinikayya tsakaninta da kungiyar tarayyar Turai ta EU, hukumar gudanarwar kungiyar ta sanar da matakin kara harajin kaso 38.1 bisa dari, kan motoci masu amfani da lantarki kirar kasar Sin ko EVs da ake shigarwa kasashe mambobin kungiyar, matakin da ko shakka babu zai yi tarnaki ga kyakkyawar alakar raya tattalin arziki dake tsakanin Sin da EU.

Kafin sanar da matakin na EU dai, kungiyar ta yi zargin cewa kamfanonin kirar motoci samfurin EVs na kasar Sin na samun rangwame daga gwamnati, don haka EU ke ganin wajibi ne ta karawa sashen haraji domin cike gibin cinikayyar motocin.

  • Xi Jinping: Sin Za Ta Ci Gaba Da Kasancewa Cikin Rukunin Kasashe Masu Tasowa
  • Sojojin Nijeriya Sun Kashe Ƴan Bindigar Daji A Dajin Taraba, Sun Ƙwato Makamai Da Kayan Aiki

To sai dai masu fashin baki da dama na ganin wannan batu na kara haraji na da nasaba da siyasa, ba wai tsantsar harkar tattalin arziki ba ne. Hakan ne ma ya sanya, da yawa daga kamfanonin kirar motoci na Turai suka bayyana adawa da wannan anniya ta kara haraji kan motocin EVs kirar kasar Sin.

Kaza lika, a matsayinsu na manyan budaddun kasuwanni, kuma masu taka muhimmiyar rawa a fannin dunkulewar duniya, Sin da EU na da masana’antu, kuma suna rarraba hajojinsu zuwa sassan duniya daban daban, a wani yanayin dake hade da juna, ta yadda zai yi wuya a iya raba tsakanin hada-hadar da suka jima suna gudanarwa tare.

Ana iya ganin wannan alaka a sashen cinikayyar motoci tsakanin sassan biyu. Alal misali, motocin da ake kerawa a Turai na samun matukar karbuwa a kasuwannin Sin. Yayin da a daya hannun, kamfanonin kera motoci na Sin suka shafe tsawon shekaru suna zuba jari, da daga matsayin fasahohinsu na kirkire-kirkire, har suka kai matsayin shiga takara mai inganci a fannin samar da motoci samfurin EVs, wadanda kasuwarsu ke matukar habaka yanzu haka a Turai.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Don haka dai ya kamata bangaren EU ya yi karatun ta nutsu, ya yi watsi da matakai na kariyar cinikayya, domin aiwatar da hakan ba abun da zai haifar sai koma baya. Kuma wannan mataki da wasu tsirarun ’yan siyasar Turai ke yayatawa, zai jefa al’ummun kasashensu cikin mawuyacin halin tsadar hajoji a wannan fanni, da rage damar su ta more kyakkyawar rayuwa.

Har ila yau, matakin karin harajin zai iya nuna rashin tabbas game da manufar da EU ta ce tana kai, ta sauya akala zuwa ga samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da shawo kan kalubalen sauyin yanayi. Ya dace EU ta yi nazari sosai, ta sauya matsaya domin kaucewa “Haihuwar ‘Da Maras Ido”! (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BRICSEUNATO
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Shirin EU Na Kakaba Karin Haraji Kan Motoci Masu Amfani Da Lantarki Kirar Sin Bai Samu Karbuwa Ba?

Next Post

Tsadar Rayuwa A Babbar Sallah: Yadda Magidanta Ke Sama Wa Kansu Mafita

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

14 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

15 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

17 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

18 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

19 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

20 hours ago
Next Post
Tsadar Rayuwa A Babbar Sallah: Yadda Magidanta Ke Sama Wa Kansu Mafita

Tsadar Rayuwa A Babbar Sallah: Yadda Magidanta Ke Sama Wa Kansu Mafita

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

July 12, 2025
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

July 12, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

July 12, 2025
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.