ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Wajaba EU Ta Dawo Daga Rakiyar Matakan Gurgunta Tsarin Cinikayya

by CGTN Hausa
2 years ago
EU

Duk da kiraye-kiraye da kasar Sin ta rika yi don gane da bukatar warware takaddamar cinikayya tsakaninta da kungiyar tarayyar Turai ta EU, hukumar gudanarwar kungiyar ta sanar da matakin kara harajin kaso 38.1 bisa dari, kan motoci masu amfani da lantarki kirar kasar Sin ko EVs da ake shigarwa kasashe mambobin kungiyar, matakin da ko shakka babu zai yi tarnaki ga kyakkyawar alakar raya tattalin arziki dake tsakanin Sin da EU.

Kafin sanar da matakin na EU dai, kungiyar ta yi zargin cewa kamfanonin kirar motoci samfurin EVs na kasar Sin na samun rangwame daga gwamnati, don haka EU ke ganin wajibi ne ta karawa sashen haraji domin cike gibin cinikayyar motocin.

  • Xi Jinping: Sin Za Ta Ci Gaba Da Kasancewa Cikin Rukunin Kasashe Masu Tasowa
  • Sojojin Nijeriya Sun Kashe Ƴan Bindigar Daji A Dajin Taraba, Sun Ƙwato Makamai Da Kayan Aiki

To sai dai masu fashin baki da dama na ganin wannan batu na kara haraji na da nasaba da siyasa, ba wai tsantsar harkar tattalin arziki ba ne. Hakan ne ma ya sanya, da yawa daga kamfanonin kirar motoci na Turai suka bayyana adawa da wannan anniya ta kara haraji kan motocin EVs kirar kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Kaza lika, a matsayinsu na manyan budaddun kasuwanni, kuma masu taka muhimmiyar rawa a fannin dunkulewar duniya, Sin da EU na da masana’antu, kuma suna rarraba hajojinsu zuwa sassan duniya daban daban, a wani yanayin dake hade da juna, ta yadda zai yi wuya a iya raba tsakanin hada-hadar da suka jima suna gudanarwa tare.

Ana iya ganin wannan alaka a sashen cinikayyar motoci tsakanin sassan biyu. Alal misali, motocin da ake kerawa a Turai na samun matukar karbuwa a kasuwannin Sin. Yayin da a daya hannun, kamfanonin kera motoci na Sin suka shafe tsawon shekaru suna zuba jari, da daga matsayin fasahohinsu na kirkire-kirkire, har suka kai matsayin shiga takara mai inganci a fannin samar da motoci samfurin EVs, wadanda kasuwarsu ke matukar habaka yanzu haka a Turai.

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

Don haka dai ya kamata bangaren EU ya yi karatun ta nutsu, ya yi watsi da matakai na kariyar cinikayya, domin aiwatar da hakan ba abun da zai haifar sai koma baya. Kuma wannan mataki da wasu tsirarun ’yan siyasar Turai ke yayatawa, zai jefa al’ummun kasashensu cikin mawuyacin halin tsadar hajoji a wannan fanni, da rage damar su ta more kyakkyawar rayuwa.

Har ila yau, matakin karin harajin zai iya nuna rashin tabbas game da manufar da EU ta ce tana kai, ta sauya akala zuwa ga samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da shawo kan kalubalen sauyin yanayi. Ya dace EU ta yi nazari sosai, ta sauya matsaya domin kaucewa “Haihuwar ‘Da Maras Ido”! (Saminu Alhassan)

EU
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

MASU ALAKA

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Next Post
Tsadar Rayuwa A Babbar Sallah: Yadda Magidanta Ke Sama Wa Kansu Mafita

Tsadar Rayuwa A Babbar Sallah: Yadda Magidanta Ke Sama Wa Kansu Mafita

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.