• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yau Kotun Tarayya Za Ta Yanke Hukuncin Masarautar Kano

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Masarautu, Manyan Labarai
0
Yau Kotun Tarayya Za Ta Yanke Hukuncin Masarautar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana zaman dar-dar a Kano a daidai lokacin da babbar kotun tarayya a ƙarƙashin Mai shari’a Muhammad Liman ke shirin yanke hukunci kan soke dokar masarautar Kano. Kotun dai ta tabbatar da hurumin ta a kan ƙarar da ta shafi hakkin dan Adam da Aminu Babba DanAgundi, Sarkin Dawaki Babba ya shigar yana kalubalanci dokar da majalisar dokokin jihar ta yi wa Masarautar inda ya ce hakan tauye masa hakkinsa. Waɗanda suka amsa sun hada da gwamnatin jihar Kano, da majalisar dokokin jihar, da hukumomin tsaro daban-daban.

Kotun zata yanke hukuncin ne a dai dai lokacin da ake ci gaba da tabka rigingimun siyasa kan masarautar. Gwamna Abba Yusuf ya mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano bayan ya gyara dokar Masarautar da ta soke masarautun jihar biyar. Wannan matakin dai ya tsige Aminu Ado Bayero, wanda tun daga lokacin ya ƙalubalanci gyaran.

Sarakunan biyu dai na samun goyon bayan ɓangarorin siyasa masu hamayya da juna: Aminu Ado APC ke goyon baya, da kuma Sanusi Lamido da NNPP ke marawa.

Aminu Ado wanda a yanzu jami’an tsaro ke ba shi kariya, yana zaune ne a kusa da gidan gwamnati, yayin da magoya bayan Gwamna Yusuf suka mamaye fadar Sarkin domin nuna goyon bayansu ga Sanusi Lamido II.

Rikicin shari’a da dama dai na faruwa a kan masarautar, ciki har da hukuncin wata babbar kotun tarayya da ta yanke biyan Aminu Ado diyyar Naira miliyan 10 bisa zargin daurin gidan da aka yi masa.

Labarai Masu Nasaba

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Yayin da kotu ke yanke hukunci kan makomar sabuwar dokar masarautar, babban lauyan gwamnatin Kano, Haruna Isah Dederi ya zargi wasu bangarori da yunƙurin hukunta jihar bisa rashin adalci. Ya jaddada aniyar gwamnatin jihar na daukaka kara kan hukuncin da kotun tarayya ta yanke na diyyar, yana mai cewa ba a tauye hakkin Aminu Ado ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alh. Aminu Ado BayeroBayerokanoKotuSunusi Lamido
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alhajin Jihar Jigawa Ya Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta Ga Mai Shi A Makka

Next Post

Dalilin Da Yasa Muke Kwace Kaddarorin Manyan Dillalan Kwaya – Buba Marwa

Related

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
Manyan Labarai

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

8 hours ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

1 day ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

2 days ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

2 days ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

2 days ago
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

2 days ago
Next Post
Dalilin Da Yasa Muke Kwace Kaddarorin Manyan Dillalan Kwaya – Buba Marwa

Dalilin Da Yasa Muke Kwace Kaddarorin Manyan Dillalan Kwaya - Buba Marwa

LABARAI MASU NASABA

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.