ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Gwamnoni Arewa Maso Yamma Za Su Yi Taro Domin Neman Mafita A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
Tsaro

Gwamnonin Arewa Maso Yamma haɗin gwiwa da hukumar UNDP za su shirya wani taron neman mafita a kan matsalar tsaro da yankin ke fama da ita shekara da shekaru.

Taron wanda ake sa ran shugaban Kasa Bola Ahmad Tunibu zai buɗe a ranar Litinin na da nufin tattaunawa da kuma lalubo hanyar da za a magance wannan matsala.

  • Harajin Da EU Ta Sanyawa Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Kasar Sin, Ita Zai Yi Wa Illa
  • Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

Taken wannan taro dai shine ‘Haɗin kan yanki domin ceton rayuka da kuma dukiyoyin al’umma”

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a wajen taron manema labarai a Katsina kwamishinan yaɗa labarai da al’adu Hon. Salisu Bala Zango ya bayyana cewa wannan taron irin sa na farko za a yi a tarihi.

Ya ƙara da cewa gwamnoni da masu ruwa da tsaki da masana daga yankin arewa maso yamma za su taro domin tattaunawa ta musamman da nufin samar da mafita akan sha’anin tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

A cewar sa, matsalar ta kai matsala ta yadda ‘yan bindiga sun hana yankin arewa maso yamma yin noma, wanda hakan ke bada gudunmawa wajen shiga kuncin rayuwa da kuma yunwa a yankin arewa da ƙasa baki ɗaya.

“Wannan taro zai maida hankali wajen ganin jihohin Kaduna da Kano da Katsina da Kebbi da Sokoto Jigawa da kuma Zamfara sun samu mafita domin yin barci da idanu biyu.” Inji shi

Kwamishinan wanda ya ƙara da cewa taron kachokam zai maida hankali ne wajan samar da yanayin mai kyau akan matsalar tsaro da kuma duba da hanyar samar da zaman lafiya mai ɗorawa ta hanyar haɗa hannun a tsakanin gwamnoni yankin.

Dakta Salisu Bala Zango ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya da gwamnonin arewa maso yamma da hukumar UNDP za su yi tattaunawa ta ilimi wajen samar da mafita a wannan yanki da matsalar tsaro ta kasra shi.

“Sannan a ƙarshen taron za a fito da musababbin matsalar tsaro da kuma tabbatar da haɗin kan jami’an tsaro da ƙoƙarin tabbatar da ingancin tsaro da hanyar za a taimakawa waɗanda bala’in ‘yan bindiga ya shafa” inji Kwamishina

Za dai a fara wannan taro a ranar Litinin a kammala ranar talata tare da fatan cewa taron zai haifar da ɗa mai ido, domin an sha yin tarurruka akan sha’anin tsaro daga baya kuma aji shiru.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
Labarai

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
Labarai

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
'yansanda
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Next Post
Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Najeriya Sun Gana A Beijing

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Najeriya Sun Gana A Beijing

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.