ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Najeriya Sun Gana A Beijing

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi, ya yi shawarwari tare da ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, jiya Jumma’a a Beijing.

Wang Yi ya ce, Najeriya babbar kasa ce a Afirka dake taka muhimmiyar rawa a fannoni daban-daban, kuma tana da matukar muhimmanci a cikin harkokin diflomasiyyar kasar Sin, gami da mu’amalarta da kasashen Afirka. Ya ce raya dangantakar kasashen biyu da kyau, ya dace da muradun al’ummominsu baki daya, kuma zai kafa wani kyakkyawan misali ga raya dangantakar kasar Sin da kasashen Afirka. Haka kuma, kasar Sin na fatan kasashen biyu za su ci gaba da marawa juna baya, da neman cimma moriya tare, da kiyaye zaman adalci da daidaito, tare da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, don neman ci gaba cikin hadin-gwiwa, da ciyar da dangantakar Sin da Najeriya, har ma da Afirka, zuwa sabon matsayi.

  • ASUU Ta Ƙalubalanci Naɗa Yan Siyasa A Matsayin Shugabannin Gudanarwar Jami’oin
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Ci Bashin Dala Miliyan 500 Don Gina Hanyoyin Karkara

A nasa bangaren, Yusuf Maitama Tuggar ya ce, Najeriya za ta ci gaba da yin tsayin daka kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana, tana fatan inganta mu’amala da manyan jami’an gwamnatin kasar Sin, da zurfafa tuntubar juna, da kara fadada hadin-gwiwarsu. Ya ce Najeriya tana kuma fatan hada kai da kasar Sin, don ingiza hadin-gwiwar kasashe masu tasowa, da tsayawa ga ra’ayin bunkasuwar bangarori daban-daban a duniya, da tabbatar da zaman adalci da tsare gaskiya a duniya.

ADVERTISEMENT

Har wa yau, jami’an biyu sun kuma halarci cikakken zama na farko na kwamitocin gwamnatocin Sin da Najeriya, wanda aka yi jiya Jumma’a a Beijing, inda suka saurari rahotannin da kwamitin bangarori daban-daban na kasashen biyu suka gabatar, ciki har da siyasa, da diflomasiyya, da al’adu, da yawon shakatawa, da tattalin arziki, da cinikayya, da sana’ar noma, da tsaro da sauransu, tare kuma da tsara shirye-shiryen hadin-gwiwar kasashen biyu a nan gaba.

Wang Yi ya bayyana cewa, kwamitin gwamnatocin kasashen Sin da Najeriya, ya kasance irinsa na farko da kasar Sin ta kafa tare da kasashen Afirka, kuma ya dace bangarorin biyu su kara fahimtar ayyukan da za su yi, da sanya muhimman ra’ayoyi iri daya da aka cimma tsakanin shugabannin kasashen biyu a gaban komai, da daukar matakai a zahirance don kara cimma nasarori.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Shi kuma minista Tuggar ya yaba sosai da nasarorin da aka cimma a zaman taron na wannan karo, inda ya ce, Najeriya tana fatan ci gaba da zurfafa fahimtar juna da kasar Sin, don cimma karin nasarori a hadin-gwiwarsu a fannoni daban-daban.

Bayan taron, bangarorin biyu sun fitar da sanarwa cikin hadin-gwiwa game da cikakken zamansu karo na farko. (Murtala Zhang)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu

Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.