ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Najeriya Sun Gana A Beijing

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi, ya yi shawarwari tare da ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, jiya Jumma’a a Beijing.

Wang Yi ya ce, Najeriya babbar kasa ce a Afirka dake taka muhimmiyar rawa a fannoni daban-daban, kuma tana da matukar muhimmanci a cikin harkokin diflomasiyyar kasar Sin, gami da mu’amalarta da kasashen Afirka. Ya ce raya dangantakar kasashen biyu da kyau, ya dace da muradun al’ummominsu baki daya, kuma zai kafa wani kyakkyawan misali ga raya dangantakar kasar Sin da kasashen Afirka. Haka kuma, kasar Sin na fatan kasashen biyu za su ci gaba da marawa juna baya, da neman cimma moriya tare, da kiyaye zaman adalci da daidaito, tare da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, don neman ci gaba cikin hadin-gwiwa, da ciyar da dangantakar Sin da Najeriya, har ma da Afirka, zuwa sabon matsayi.

  • ASUU Ta Ƙalubalanci Naɗa Yan Siyasa A Matsayin Shugabannin Gudanarwar Jami’oin
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Ci Bashin Dala Miliyan 500 Don Gina Hanyoyin Karkara

A nasa bangaren, Yusuf Maitama Tuggar ya ce, Najeriya za ta ci gaba da yin tsayin daka kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana, tana fatan inganta mu’amala da manyan jami’an gwamnatin kasar Sin, da zurfafa tuntubar juna, da kara fadada hadin-gwiwarsu. Ya ce Najeriya tana kuma fatan hada kai da kasar Sin, don ingiza hadin-gwiwar kasashe masu tasowa, da tsayawa ga ra’ayin bunkasuwar bangarori daban-daban a duniya, da tabbatar da zaman adalci da tsare gaskiya a duniya.

ADVERTISEMENT

Har wa yau, jami’an biyu sun kuma halarci cikakken zama na farko na kwamitocin gwamnatocin Sin da Najeriya, wanda aka yi jiya Jumma’a a Beijing, inda suka saurari rahotannin da kwamitin bangarori daban-daban na kasashen biyu suka gabatar, ciki har da siyasa, da diflomasiyya, da al’adu, da yawon shakatawa, da tattalin arziki, da cinikayya, da sana’ar noma, da tsaro da sauransu, tare kuma da tsara shirye-shiryen hadin-gwiwar kasashen biyu a nan gaba.

Wang Yi ya bayyana cewa, kwamitin gwamnatocin kasashen Sin da Najeriya, ya kasance irinsa na farko da kasar Sin ta kafa tare da kasashen Afirka, kuma ya dace bangarorin biyu su kara fahimtar ayyukan da za su yi, da sanya muhimman ra’ayoyi iri daya da aka cimma tsakanin shugabannin kasashen biyu a gaban komai, da daukar matakai a zahirance don kara cimma nasarori.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Shi kuma minista Tuggar ya yaba sosai da nasarorin da aka cimma a zaman taron na wannan karo, inda ya ce, Najeriya tana fatan ci gaba da zurfafa fahimtar juna da kasar Sin, don cimma karin nasarori a hadin-gwiwarsu a fannoni daban-daban.

Bayan taron, bangarorin biyu sun fitar da sanarwa cikin hadin-gwiwa game da cikakken zamansu karo na farko. (Murtala Zhang)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

MASU ALAKA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
Next Post
Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu

Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.