ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Najeriya Sun Gana A Beijing

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi, ya yi shawarwari tare da ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, jiya Jumma’a a Beijing.

Wang Yi ya ce, Najeriya babbar kasa ce a Afirka dake taka muhimmiyar rawa a fannoni daban-daban, kuma tana da matukar muhimmanci a cikin harkokin diflomasiyyar kasar Sin, gami da mu’amalarta da kasashen Afirka. Ya ce raya dangantakar kasashen biyu da kyau, ya dace da muradun al’ummominsu baki daya, kuma zai kafa wani kyakkyawan misali ga raya dangantakar kasar Sin da kasashen Afirka. Haka kuma, kasar Sin na fatan kasashen biyu za su ci gaba da marawa juna baya, da neman cimma moriya tare, da kiyaye zaman adalci da daidaito, tare da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, don neman ci gaba cikin hadin-gwiwa, da ciyar da dangantakar Sin da Najeriya, har ma da Afirka, zuwa sabon matsayi.

  • ASUU Ta Ƙalubalanci Naɗa Yan Siyasa A Matsayin Shugabannin Gudanarwar Jami’oin
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Ci Bashin Dala Miliyan 500 Don Gina Hanyoyin Karkara

A nasa bangaren, Yusuf Maitama Tuggar ya ce, Najeriya za ta ci gaba da yin tsayin daka kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana, tana fatan inganta mu’amala da manyan jami’an gwamnatin kasar Sin, da zurfafa tuntubar juna, da kara fadada hadin-gwiwarsu. Ya ce Najeriya tana kuma fatan hada kai da kasar Sin, don ingiza hadin-gwiwar kasashe masu tasowa, da tsayawa ga ra’ayin bunkasuwar bangarori daban-daban a duniya, da tabbatar da zaman adalci da tsare gaskiya a duniya.

ADVERTISEMENT

Har wa yau, jami’an biyu sun kuma halarci cikakken zama na farko na kwamitocin gwamnatocin Sin da Najeriya, wanda aka yi jiya Jumma’a a Beijing, inda suka saurari rahotannin da kwamitin bangarori daban-daban na kasashen biyu suka gabatar, ciki har da siyasa, da diflomasiyya, da al’adu, da yawon shakatawa, da tattalin arziki, da cinikayya, da sana’ar noma, da tsaro da sauransu, tare kuma da tsara shirye-shiryen hadin-gwiwar kasashen biyu a nan gaba.

Wang Yi ya bayyana cewa, kwamitin gwamnatocin kasashen Sin da Najeriya, ya kasance irinsa na farko da kasar Sin ta kafa tare da kasashen Afirka, kuma ya dace bangarorin biyu su kara fahimtar ayyukan da za su yi, da sanya muhimman ra’ayoyi iri daya da aka cimma tsakanin shugabannin kasashen biyu a gaban komai, da daukar matakai a zahirance don kara cimma nasarori.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Shi kuma minista Tuggar ya yaba sosai da nasarorin da aka cimma a zaman taron na wannan karo, inda ya ce, Najeriya tana fatan ci gaba da zurfafa fahimtar juna da kasar Sin, don cimma karin nasarori a hadin-gwiwarsu a fannoni daban-daban.

Bayan taron, bangarorin biyu sun fitar da sanarwa cikin hadin-gwiwa game da cikakken zamansu karo na farko. (Murtala Zhang)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu

Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.