• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Kasar Zimbabwe Ya Aure Mahaifiyarsa Bayan Ya Yi Mata Ciki

by Leadership Hausa
1 year ago
in Al'ajabi
0
Dan Kasar Zimbabwe Ya Aure Mahaifiyarsa Bayan Ya Yi Mata Ciki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata uwa ‘yar kasar Zimbabwe da danta sun yi ikirarin cewa suna soyayya da juna kuma sun yanke shawarar su yi aure bisa la’akari da cewa mahaifiyar Betty Mbereko (daga Mwenezi a Masbingo) tana da ciki wata shida a yanzu kuma tana jiran haihuwar abin da ke cikinta wanda zai zama danta kuma jikanta.

Mbereko, mai shekaru 40, ta kasance bazawara tun shekaru 12 da suka gabata inda take zaune da danta mai shekaru 23 mai suna Farai Mbereko.

  • Gwamnan Kano Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Kawo Karshen Fadan Daba A Kano
  • Harajin Da EU Ta Sanyawa Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Kasar Sin, Ita Zai Yi Wa Illa

Ta tabbatar da cewa tana da ciki wata shida kuma ta yanke shawarar cewa zai fi kyau ta “aure” danta domin ba ta son auren ’yan’uwan mijinta da ya rasu, wadanda ta ce suna matukar kwadayin ganin sun aure ta.

Betty ta girgiza wata kotun akuye a makon da ya gabata lokacin da ta ce ta fara kaunar dan nata ne a matsayin wanda za ta iya aura tun shekaru uku da suka wuce. Ta ce bayan kashe makudan kudade ta tura Farai makaranta bayan rasuwar mijinta, don haka ta ji cewa tana da hakki a kan kudin da yake samu yanzu domin babu wata mace da ta cancanci hakan.

“Duba da cewa, ni kadai na yi ta fama da gwagwarmaya don in tura dana makaranta, ba wanda ya taimake ni. Yanzu ka ga dana yana aiki kuma don na ce zan aure shi sai ka zarge ni da aikata ba daidai ba?

Labarai Masu Nasaba

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

“A bar ni kawai in ji dadin gumina da na barje,” ta fada wa kotun kauyen.

A nashi bangaren, dan nata, Farai ya ce shi kansa ya fi son ya aure mahaifiyarsa kuma zai biya ragowar bashin sadakin da mahaifinsa ya gadar wa a kakanninsa.

“Na san mahaifina ya rasu kafin ya gama biyan kudin sadaki kuma a shirye nake in biya,” in ji shi.

“Yana da kyau a bayyana abin da ke faruwa domin mutane su sani cewa ni ne na yi wa mahaifiyata ciki. Idan ba haka ba, za su tuhume ta da fasikanci.”

Sai dai kuma, Dagacin kauyen, Nathan Muputirwa ya ce: “Ba za mu kyale hakan ya faru a kauyenmu ba, domin hakika wannan mummunan al’amari ne). Idan da a zamanin baya suka yi hakan dole ne a zartar musu da hukuncin kisa amma a yau ba za mu iya ba saboda muna tsoron ‘yansanda.”

Ya gargade su da su gaggauta yanke wannan kudiri na auren junansu ko kuma su bar kauyen da zama.

Tuni dai majiyarmu ta bayyana cewa uwar da dan sun zabi su yi hijira daga kauyen inda suka koma wani wuri da ba a bayyana ba.

Majiya: One Africa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AureƊaMahaifiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Isra’ila Ta Sake Kai Hari, Ta Halaka Yara Kanana Falasɗinawa 5 A Yankunan Fararen-hula A Gaza

Next Post

Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza – Majalisar Dinkin Duniya

Related

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

2 weeks ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

3 weeks ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

1 month ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

2 months ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

2 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

3 months ago
Next Post
Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza – Majalisar Dinkin Duniya

Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza - Majalisar Dinkin Duniya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

July 12, 2025
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

July 12, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

July 12, 2025
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.