ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza – Majalisar Dinkin Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Gaza

Hukumar kare hakkin bil’Adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana ganin Isra’ila na ci gaba da saba dokokin duniya a ruwan bama-bamai da take yi a Gaza.

Hukumar ta yi nazari a kan wasu hare-haren bam shida da Isra’ilar ta kai a shekarar da ta wuce, wadanda ta kai gidajen jama’a da makaranta da sansanonin an gudun hijira da kuma wata kasuwa.

  • Muhimmiyar Takarda Kan Yanke Hukunci Mai Tsanani Kan Masu Yunkurin Balle Taiwan Daga Kasar Sin Ta Bullo Da Wasu Sakwanni Uku
  • Firaministan Kasar Kyrgyzstan: Layin Dogon Da Ya Hada Kasashen Sin Da Kyrgyzstan Da Uzbekistan Zai Taimaka Ga Raya Kyrgyzstan Har Ta Zama Mahadar Jigilar Hajoji

Ta ce, manyan makaman da aka yi amfani da su ba za su iya tantance tsakanin farar hula da mayaka ba, saboda haka babu dalilin yin amfani da su a wuraren.

ADVERTISEMENT

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta tabbatar da mutuwar mutum 218 a hare-haren amma tana ganin yawan ma ya fi haka.

Babban Jami’in Kula da Hakkin Dan’Adam na Majalisar, Bolker Turk, ya ce hare-haren bom na Isra’ila ka iya zama laifukan cin zarafin bil’Adama.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

Al’ummar Zirin Gaza na cikin mawuyacin hali na mummunar illa ga lafiya da kuma muhallinsu saboda yakin da Isra’ila ke yi da Hamas ya tilasta musu zama cikin kazanta.

Asmahan al-Masri, wacce ta yi gudun hijira daga Beit Hanoun, yanzu tana zaune a Khan Younis, ta bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin kisan mummuke, inda ta koka da cututtukan da jikokinta ke fama da su, wadanda suka hada da karzuwa.

A cikin wata takwas da ya gabata, fiye da tan 330,400 na bola aka tara a Gaza, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin agaji suka bayyana.

Mutum 16 na dangin Masri na cunkushe a cikin wani tanti kusa da jami’ar al-Aksa, kewaye da kudaje da karnuka da warin sharar da ta rube.

Mawuyacin hali ya tilasta wa mutane da yawa, kamar Mohamed, kalen abinci da sauran tarkace domin sayarwa don su rayu.

Sama da mutum miliyan daya da suka tsere daga harin da sojojin Isra’ila suka kai a Rafah yanzu haka suna zaune a yankunan da suka koma wurin tara shara na wucin-gadi.

Ali Nasser, wanda kwanan nan ya koma sansanin jami’ar al-Aksa daga Rafah, ya bayyana irin halin da suke ciki da suka hada da larurar amai da gudawa, da kuma karzuwa saboda rashin kyawun rayuwa.

Shekaru da dama da Isra’ila da Masar suka yi na killace yankin ya haifar da cikas ga ayyukan yau da kullum kamar zubar da shara a Gaza.

Tun bayan harin da Hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba, sojojin Isra’ila suka toshe hanyoyin shiga manyan wuraren da ake zubar da shara a Gaza, lamarin da ya ta’azzara rikicin.

A cewar Sam Rose, darektan tsare-tsare na hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Falasdinawa UNRWA, yanayin kula da shara a Gaza ya tabarbare matuka.

Hotunan shafukan intanet da binciken da BBC Berify ta yi sun nuna yadda ake samun yawan zubar da shara barkatai, yayin da mutane ke tserewa zuwa garuruwa da birane daban-daban.

Yawancin wuraren kula da ruwa da bahaya sun lalace.

Gaza
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

LABARAI MASU NASABA

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.