ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza – Majalisar Dinkin Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Gaza

Hukumar kare hakkin bil’Adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana ganin Isra’ila na ci gaba da saba dokokin duniya a ruwan bama-bamai da take yi a Gaza.

Hukumar ta yi nazari a kan wasu hare-haren bam shida da Isra’ilar ta kai a shekarar da ta wuce, wadanda ta kai gidajen jama’a da makaranta da sansanonin an gudun hijira da kuma wata kasuwa.

  • Muhimmiyar Takarda Kan Yanke Hukunci Mai Tsanani Kan Masu Yunkurin Balle Taiwan Daga Kasar Sin Ta Bullo Da Wasu Sakwanni Uku
  • Firaministan Kasar Kyrgyzstan: Layin Dogon Da Ya Hada Kasashen Sin Da Kyrgyzstan Da Uzbekistan Zai Taimaka Ga Raya Kyrgyzstan Har Ta Zama Mahadar Jigilar Hajoji

Ta ce, manyan makaman da aka yi amfani da su ba za su iya tantance tsakanin farar hula da mayaka ba, saboda haka babu dalilin yin amfani da su a wuraren.

ADVERTISEMENT

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta tabbatar da mutuwar mutum 218 a hare-haren amma tana ganin yawan ma ya fi haka.

Babban Jami’in Kula da Hakkin Dan’Adam na Majalisar, Bolker Turk, ya ce hare-haren bom na Isra’ila ka iya zama laifukan cin zarafin bil’Adama.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Al’ummar Zirin Gaza na cikin mawuyacin hali na mummunar illa ga lafiya da kuma muhallinsu saboda yakin da Isra’ila ke yi da Hamas ya tilasta musu zama cikin kazanta.

Asmahan al-Masri, wacce ta yi gudun hijira daga Beit Hanoun, yanzu tana zaune a Khan Younis, ta bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin kisan mummuke, inda ta koka da cututtukan da jikokinta ke fama da su, wadanda suka hada da karzuwa.

A cikin wata takwas da ya gabata, fiye da tan 330,400 na bola aka tara a Gaza, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin agaji suka bayyana.

Mutum 16 na dangin Masri na cunkushe a cikin wani tanti kusa da jami’ar al-Aksa, kewaye da kudaje da karnuka da warin sharar da ta rube.

Mawuyacin hali ya tilasta wa mutane da yawa, kamar Mohamed, kalen abinci da sauran tarkace domin sayarwa don su rayu.

Sama da mutum miliyan daya da suka tsere daga harin da sojojin Isra’ila suka kai a Rafah yanzu haka suna zaune a yankunan da suka koma wurin tara shara na wucin-gadi.

Ali Nasser, wanda kwanan nan ya koma sansanin jami’ar al-Aksa daga Rafah, ya bayyana irin halin da suke ciki da suka hada da larurar amai da gudawa, da kuma karzuwa saboda rashin kyawun rayuwa.

Shekaru da dama da Isra’ila da Masar suka yi na killace yankin ya haifar da cikas ga ayyukan yau da kullum kamar zubar da shara a Gaza.

Tun bayan harin da Hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba, sojojin Isra’ila suka toshe hanyoyin shiga manyan wuraren da ake zubar da shara a Gaza, lamarin da ya ta’azzara rikicin.

A cewar Sam Rose, darektan tsare-tsare na hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Falasdinawa UNRWA, yanayin kula da shara a Gaza ya tabarbare matuka.

Hotunan shafukan intanet da binciken da BBC Berify ta yi sun nuna yadda ake samun yawan zubar da shara barkatai, yayin da mutane ke tserewa zuwa garuruwa da birane daban-daban.

Yawancin wuraren kula da ruwa da bahaya sun lalace.

Gaza
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

Matar Tsohon Shugaban ISIS, Al-Baghdadi Ta Bayyana Wasu Sirrika

LABARAI MASU NASABA

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

July 20, 2026
Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana

Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana

July 20, 2026
Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

July 20, 2026
ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

July 20, 2026
Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

July 20, 2026
Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

July 20, 2026
Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.