• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wuraren Tarihi Da Suka Kamata Alhazai Su Ziyarta A Makkah Da Madinah

by Bello Hamza
11 months ago
in Labarai
0
Wuraren Tarihi Da Suka Kamata Alhazai Su Ziyarta A Makkah Da Madinah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai wuraren ajiye kayan tarihi masu dama da miliyoyin musulmi ke turuwar zuwa domin ilimantar da kasu a garin Al-Makkatu Mukarramah da Madinah Al-Munawara a duk shekara.

Bayan kammala ayyukan ibada na Umara ko Hajji tare da gudanar da dawafi da sa’ayi, alhazai kan kuma kosa su ziyarci wasu wurare masu muhimmanci a tarihin addinin musulunci.

  • Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya
  • Summer Davos: An Tattauna “Sababbin Damammaki A Kasar Sin”

Garuruwan biyu nada tarihin da ya wuce dubban shekaru, sun kuma danfaru da tarihin addnin musuluncin ne gaba daya, za kuma su ga yadda wasu al’adu da gine-ginen garuruwan suka canza a tsawon shekarun da suka wuce.

Wuri na farko da ya kamata Alhaji ya ziyarta shi ne unguwar da ake kira da ‘Unguwar Al’adu ta Hira’.

Domin fahimtar tarihi da muhimmancin wadannan garuruwan, dole mai ziyara ya yi nazarin muhimmancin su ga addinin musulunci, ana shawartar Alhazai su samu ziyartar wurare kamar Jannat Ul Mua’lla, Kogon Hira a kan dutsen ‘Jabal Al-Nour’, Dutsen Arafat da masallacin Ayesha.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

Haka kuma a kusa da masallacin Haram akwai wuri mai muhimmanci da aka fi sani da Hudaibiyah, wurin da Manzo (SAW) ya sanya hannu a yarjejeniyar Hudaibiyah. Domin taskace tarihi da muhimmancin wurin a yanzu an gina masallaci a daidai wurin.

A shekarar 809, lokacin da aka fuskanci tsananin rashin ruwa a garin Makkah, Sarauniya Zubaida, matar Kalipha Harun Rashid, ta tafi aikin hajji, inda ta lura da wahalar da al’umma ke fama na rashin ruwa, a kan haka ta bayar da umarnin gina tafkin da aka fi sani da ‘Zubaida Canal’.

Yanzu shekaru dubbai ke nan alhazai na ci gaba da amfana da ruwan da ke fitowa daga tafkin.

Sai kuma dutsen Abu Kubais, inda mu’ujizar nan na wata ya faru, zai kuma ci gaba da kasancewa wani abin tunatarwa game da mu’ijizozin addinin musulunci.

Wani wurin da ya kamata alhaji ya ziyarta shi ne gidan tarihi na “Assalaamu Aleyka Ayyuhan Nabiyyu” a nan masu ziyara za su gani a bayyane tarihin rayuwar Annabi Muhammadu (SAW), ta hanyar kayayyakin da ya yi amfani da su a lokacin yana raye za su samu damar fahimmatar rayuwarsa da na kakanninsa, matansa, yaransa da sauran abubuwan da suka shafi gwagwarmayarsa ta tabbatar da addini. An kafa wannan gidan tarihi ne da hadin gwiwar malamai da masana fiye da 150 domin tabbatar da inganci da sahihancin abubuwan da aka samar a gidan.

Wani mai suna Ahmed Khanya ya bayyana cewa, shekararsa 15 yana aikin zagayawa da Alhazai wurare masu tsarki a garuwar Makkah da Madina.

“A kodayaushe Alhazai na jin dadin ziyartar wuraren da ke tattare da tarihin Manzon Tsira Muhammad Dan Abdullahi wanda hakan ke taimaka musu samun cikakkiyar fahimtar tarin addinin musulunci.”

Wasu wuraren sun kuma hada da kogon Hira a nan ne Manzon Allah (SAW) da Sahabinsa Abubakar suka boye a lokacin da Kuraishawa suka kai musu hari a yayin da suke hijira zuwa Madinah.

A garin Madinah, wanda ita ce ta biyu a daraja, musulmi shaukin ziyartar wuraren tarihi a garin da suka hada da, Masjid Al-Kiblatain, Masjid Abu Bakr, Masjid Al-Ahzab haka kuma akwai Masjid Al-Ghamamah duk da kankancinsa yana da muhimmanci don neman albarka a garin Madinah. Akwai kuma makabartar Baki’a da filin da aka tafka yakin Uhud.

Haka kuma akwai wuraren da aka yi wasu yake-yake masu matukar tarihi a addnini musulunci kamar yakin Khandak da aka yi a shekara ta 624 bayan hijira, a halin yanzu an gina babban masallaci a daidai wurin da aka yi yakin a tsakanin Musulman Madinah da Mushirikan Makkah.

Akwai kuma gonar Sayiddina Salman Farsi a Madinah inda tarihi ya nuna cewa, Manzon Allah (SAW) ya shuka dabino fiye da 300 domin ya ‘yantar da Salman Farsi daga bauta, daga nan kuma sai masallacin Kuba.

Ga wanda ya samu ikon zuwa kasa mai tsarki domin gudanar da ibadar Umara ko aikin Hajji ya kamata ya nemi a kai shi ziyara wadanna wuraren domin suna kara wa mutum Imani da fahimtar addninin musulunci, zai kuma fahimci irin canje-canje da aka samu a tsawon shekarun da suka wuce.

 

Yadda Aka Yi Dawafi Da Kananan Motoci A Hajjin Bana

Hukumar kula da harkokin masallaci mai alfarma da masallacin Manzo (SAW) ta kaddamar da yin dawafi ta hanyar amfani da wasu kananann motoci domin amfani da Alhazawa masi bukata ta musamman da kuma attajirai.

An jibge motocin ne a kofar shiga ta ‘Ajyad Escalators’ da ‘King Abdulaziz Gate Elebators’ da kuma ‘Umrah Gate Elebators’ ta yadda masu bukata za su gan su ba tare da wani wahala ba.

Motocin suna aiki a kullum na tsawon awa 12, daga karfe 4 na yamma zuwa karfe 4 na asuba ga duk wanda yake bukata.

Farashin hawa motar ya fara ne daga Riyal 25, ga duk mai bukatar yin dawafi ba tare da fuskantar cunkoso ba, kuma a cikin dan kankanin lokaci. Ana iya samun tikitin hawa motar a harabar Masallacin.

A wannan shekarar an yi amfani ne da kananan motoci 50 inda kowanne ke daukar mutum goma.

Saboda yawan al’umma da kuma irin cunkoson da ake fuskanta yayin gudanar da ibada, hukumomin kasar Saudiya na ci gaba da kirkiro da hanyoyin saukaka yadda ake gudanar da wasu ayyukan ibada yayin aikin hajji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HajjiSaudiyyaWuraren Tarihi
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Mahaifiyar Rarara

Next Post

Mutane 2 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Su Da Hannu A Sace Mahaifiyar Rarara

Related

katsina
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

49 minutes ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

3 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

14 hours ago
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

17 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

17 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

20 hours ago
Next Post
Mutane 2 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Su Da Hannu A Sace Mahaifiyar Rarara

Mutane 2 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Su Da Hannu A Sace Mahaifiyar Rarara

LABARAI MASU NASABA

katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.