ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

by Sadiq
11 months ago
'Yansanda

Rundunar ‘Yansandan Jihar Katsina ta sanar da kama mutane 302 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban, da kuma ceto sama da mutane 50 da aka sace a cikin watan Yulin 2025.

Kakakin ‘yansandan jihar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, wanda ya wakilci Kwamishinan ‘Yansanda, CP Bello Shehu, a taron manema labarai da aka gudanar a ranar Juma’a, ya gode wa Sufeto Janar na ‘Yansanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, bisa goyon baya da ya bayar wanda ya taimaka matuƙa wajen yaƙi da laifuka a jihar.

Ya bayyana cewa daga cikin waɗanda aka kama akwai:

ADVERTISEMENT
  • Mutum 14 da ake zargi da fashi da makami
  • Mutum 22 da ake zargi da kisa
  • Mutum 25 da ake zargi da aikata fyaɗe
  • Mutum 20 da ake zargi da lalata kayan gwamnati
  • Mutum 8 da ake zargi da damfara
  • Mutum 26 da ake zargi da sayar da miyagun ƙwayoyi
  • Mutane 194 da ake zargi da sauran laifuka daban-daban

DSP Aliyu ya ƙara da cewa rundunar ta daƙile hare-haren ‘yan fashi da dama a tsawon lokacin.

Kayan da aka ƙwato sun haɗa da:

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

  • Dabbobi 199 da aka sace (shanu 161 da tumaki 68)
  • Motoci guda 3 da aka sace
  • Babura 2 da ake zargi an sace su
  • Miyagun ƙwayoyi da yawa ciki har da tabar wiwi
  • Wayoyin wutar lantarki da aka lalata

DSP Aliyu ya yaba wa gwamnatin Jihar Katsina da al’ummar jihar saboda haɗin kai da suka bayar, yana mai cewa ba za a cimma nasarorin ba tare da taimakon jama’a ba.

Ya buƙaci al’umma su ci gaba da bai wa ‘yansanda goyon baya, tare da kai rahoton duk wani abun zargi ta waɗannan layukan gaggawa: 0815697777722, 0902220969033, da 07072722539.

“Rundunar ‘Yansandan Jihar Katsina za ta ci gaba da ƙoƙarinta don kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar,” in ji shi.

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
Next Post
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.