• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gidan Buhari Ya Zama Fadar Ziyarar Jiga-jigan ‘Yan Siyasa

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Yadda Gidan Buhari Ya Zama Fadar Ziyarar Jiga-jigan ‘Yan Siyasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gidan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke Daura a Jihar Katsina ya zama fadar ziyarar manyan ‘yan siyasar Nijeriya.

A wannan makon dai, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa a karkashin tutar jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya ziyarci Buhari a gidansa da ke Daura a Jihar Katsina, inda suka yi ganawar sirri tare da tsohon wamnan Jihar Sakkwato kuma sanata mai wakiltar Sakkwato ta kudu, Aminu Waziri Tambuwal.

  • Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya
  • Rasuwar Suruka: Gwamnoni Sun Kai Wa Shettima Ziyarar Ta’aziyya

Sai dai ba a samu cikakken bayani kan tattaunawar da fitattun ‘yan siyasar suka yi ba, amma wasu manazarta na ganin ziyarar a matsayin wata dabarar da Atiku ya dauka na tabbatar da samun nasara a zaben shugaban kasa a 2027.

Amma a wata sanarwa da ya fitar, mai bai wa Atiku shawara kan harkokin yada labarai, Mista Paul Ibe ya ce tsohon mataimakin shugaban kasar ya kai ziyarar jaje ne Jihar Katsina.

Sanarwar ta ce, “Tsohon mataimakin shugaban kasar Nijeriya kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben shugaban a 2023, Atiku Abubakar ya jagoranci sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar zuwa gidan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Alhaji Lawan Kaita a Daura wajen kai gaisuwar ta’aziyyar mutuwa da aka yi wa iyalan.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

“Ziyarar wacce ta samu kyakkyawar tarba ga Atiku a manyan garuruwan masarautar Daura, sannan tsohon mataimakin shugaban kasar ya kai irin wannan ziyarar ga Sarkin Daura, Alhaji Farouk Umar Farouk da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

“Taron da Atiku Abubakar ya yi a Jihar Katsina, ci gaba ne da ziyarar ban girma da ya kai tun bayan kammala bukukuwan Sallah da kuma jajanta wa iyalan tsohon abokinsa, Malam Lawan Kaita,” in ji shi.

Sanarwarta kara da cewa Atiku ya kuma ziyarci Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman.

Kwanaki biyar kafin tafiyar tasa zuwa Daura, tsohon mataimakin shugaban kasa ya kai ziyara daban-daban ga tsaffin shugabannin sojoji, Ibrahim Badamasi Babangida da Abdulsalami Abubakar a gidajensu Minna a babban birnin Jihar Neja.

Wannan ita ce ziyara ta farko da Atiku ya yi wa Buhari tun bayan da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zabukan 2019 da 2023 ya fice daga jam’iyyar APC.

An kuma bayyana ziyarar tsohon shugaban kasan a matsayin wani dabarar siyasa da Atiku ya dauka”, musamman a daidai lokacin da yake kokarin hadakar jam’iyyun adawa don kwace mulki a wurin jam’iyyar APC karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu a 2027.

Yunkurin nasa ya kara daukar hankali a watan da ya gabata lokacin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben bara, Peter Obi, ya kai masa ziyarar ban girma. Obi shi ne abokin takarar Atiku a zaben shugaban kasa na 2019 da suka fafata da Buhari. Bayan sa’o’i 24 da ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari, shi ma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru el-Rufai ya kai irin wannan ziyarar ga tsohon shugaban kasa a gidansa da ke Daura.

Kafin yanzu, gidajen tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo da tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Ibrahim Babangida da tsohon shugaban kasa, Abdulsalami Abubakar, ya kasance wurin da ‘yan siyasa ke tururun kai ziyara.

Sai dai gidan tsohon shugaban kasa Buhari da ke Daura na ci gaba da ganin shahararrun ‘yan siyasa, musamman daga yankin arewacin Nijeriya.

Haka kuma, shi ma tsohon gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff yana daga cikin manyan ‘yan siyasan da suka kai wa tsohon shugaban kasa Buhari ziyara a gidansa da ke Daura.

Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya soki wannan ziyarar da ‘yan siyasar arewa suke kai wa tsohon shugaban kasa Buhari. Yana mai cewa wannan wani yunkuri ne da ‘yan siyasan arewa suke yi na shirin tunkude shugaban kasa, Bola Tinubu a 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SiyasaBuhariZiyara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Bukatar Mu Bai Wa Mara Ɗa Kunya A Gasar EURO Ta Bana – Gordon

Next Post

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.