ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gidan Buhari Ya Zama Fadar Ziyarar Jiga-jigan ‘Yan Siyasa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Buhari

Gidan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke Daura a Jihar Katsina ya zama fadar ziyarar manyan ‘yan siyasar Nijeriya.

A wannan makon dai, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa a karkashin tutar jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya ziyarci Buhari a gidansa da ke Daura a Jihar Katsina, inda suka yi ganawar sirri tare da tsohon wamnan Jihar Sakkwato kuma sanata mai wakiltar Sakkwato ta kudu, Aminu Waziri Tambuwal.

  • Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya
  • Rasuwar Suruka: Gwamnoni Sun Kai Wa Shettima Ziyarar Ta’aziyya

Sai dai ba a samu cikakken bayani kan tattaunawar da fitattun ‘yan siyasar suka yi ba, amma wasu manazarta na ganin ziyarar a matsayin wata dabarar da Atiku ya dauka na tabbatar da samun nasara a zaben shugaban kasa a 2027.

ADVERTISEMENT

Amma a wata sanarwa da ya fitar, mai bai wa Atiku shawara kan harkokin yada labarai, Mista Paul Ibe ya ce tsohon mataimakin shugaban kasar ya kai ziyarar jaje ne Jihar Katsina.

Sanarwar ta ce, “Tsohon mataimakin shugaban kasar Nijeriya kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben shugaban a 2023, Atiku Abubakar ya jagoranci sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar zuwa gidan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Alhaji Lawan Kaita a Daura wajen kai gaisuwar ta’aziyyar mutuwa da aka yi wa iyalan.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

“Ziyarar wacce ta samu kyakkyawar tarba ga Atiku a manyan garuruwan masarautar Daura, sannan tsohon mataimakin shugaban kasar ya kai irin wannan ziyarar ga Sarkin Daura, Alhaji Farouk Umar Farouk da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

“Taron da Atiku Abubakar ya yi a Jihar Katsina, ci gaba ne da ziyarar ban girma da ya kai tun bayan kammala bukukuwan Sallah da kuma jajanta wa iyalan tsohon abokinsa, Malam Lawan Kaita,” in ji shi.

Sanarwarta kara da cewa Atiku ya kuma ziyarci Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman.

Kwanaki biyar kafin tafiyar tasa zuwa Daura, tsohon mataimakin shugaban kasa ya kai ziyara daban-daban ga tsaffin shugabannin sojoji, Ibrahim Badamasi Babangida da Abdulsalami Abubakar a gidajensu Minna a babban birnin Jihar Neja.

Wannan ita ce ziyara ta farko da Atiku ya yi wa Buhari tun bayan da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zabukan 2019 da 2023 ya fice daga jam’iyyar APC.

An kuma bayyana ziyarar tsohon shugaban kasan a matsayin wani dabarar siyasa da Atiku ya dauka”, musamman a daidai lokacin da yake kokarin hadakar jam’iyyun adawa don kwace mulki a wurin jam’iyyar APC karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu a 2027.

Yunkurin nasa ya kara daukar hankali a watan da ya gabata lokacin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben bara, Peter Obi, ya kai masa ziyarar ban girma. Obi shi ne abokin takarar Atiku a zaben shugaban kasa na 2019 da suka fafata da Buhari. Bayan sa’o’i 24 da ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari, shi ma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru el-Rufai ya kai irin wannan ziyarar ga tsohon shugaban kasa a gidansa da ke Daura.

Kafin yanzu, gidajen tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo da tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Ibrahim Babangida da tsohon shugaban kasa, Abdulsalami Abubakar, ya kasance wurin da ‘yan siyasa ke tururun kai ziyara.

Sai dai gidan tsohon shugaban kasa Buhari da ke Daura na ci gaba da ganin shahararrun ‘yan siyasa, musamman daga yankin arewacin Nijeriya.

Haka kuma, shi ma tsohon gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff yana daga cikin manyan ‘yan siyasan da suka kai wa tsohon shugaban kasa Buhari ziyara a gidansa da ke Daura.

Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya soki wannan ziyarar da ‘yan siyasar arewa suke kai wa tsohon shugaban kasa Buhari. Yana mai cewa wannan wani yunkuri ne da ‘yan siyasan arewa suke yi na shirin tunkude shugaban kasa, Bola Tinubu a 2027.

Buhari
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.