• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Riƙa Bincike Kafin Ku Yi Magana, Martanin Gwamnatin Katsina Ga ASUU

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
in Ilimi
0
Ku Riƙa Bincike Kafin Ku Yi Magana, Martanin Gwamnatin Katsina Ga ASUU
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Katsina ta mayar wa ƙungiyar Malaman jami’a ASUU reshen jami’ar Yar’adua da ke Katsina martani dangane da iƙirarin da ƙungiyar ta yi na cewa jami’ar ta kama hanyar durƙushewa. 

Kwamishinan ma’aikatan ilimi mai zurfi da kula da ƙere-ƙere Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya maida martanin ne da cewa ba gwamnatin su ba ce ta rage kuɗaɗen gudanarwar jami’ar ba.

“Wannan gwamnatin ƙarkashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa bata taɓa rage ko Naira ba daga kuɗaɗen gudanarwa da ake ba jami’ar Yar’adua kuma ba a taɓa fashin biyan su ba.”inji shi.

Kwamishinan wanda ya ce shi daya ne daga cikin Malaman jami’ar kafin ya samu muƙami yasan duk abinda ke faruwa yana da masaniyar musamman tafiyar da sha’anin jami’ar

  • ASUU Ta Bada Wa’adin Mako 3 Ga Gwamnatin Tarayya, Ta Yi Barazanar Shiga Sabon Yajin aiki
  • Jami’ar Yar’adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa – ASUU

Kazalika ya yi kira ga ƙungiyar ASUU da ta koma jami’ar ta bincika ta gani daga yaushe ne aka rage waɗancan kuɗaɗen da suke magana, ba wai su fito a kafafen yaɗa labarai suna faɗin abinda ba haka yake ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

Sannan ya ƙara da cewa babu wanda ya taɓa rubutawa gwamnati cewa kuɗaɗen gudanarwa da ake ba jami’ar da sauran manyan makarantu ba sa isar su, babu wanda ya taɓa sanar da gwamnati.

“Kuma ina san jama’a da su gane, ASUU sun ce adadin ɗalibai da tsangaya sun ƙaro, to su bayyanawa duniya adadin kuɗaɗen shiga da suke samu a yanzu kowa ya sani.

A cewar sa, ko Naira ɗaya basa ba gwamnatin jihar Katsina, su ke tara kuɗin su, su ke kashe su, saboda haka ya ce su je su bincika tun shekarar 2015 aka fara zabtare kuɗaɗen gudanarwa na jami’ar da sauran makarantu guda biyar.

Da kwamishinan ya juya game da korafin da ƙungiyar ASUU ta yi na cewa gwamnatin tarayya ta fara aiwatar da shirin ƙarin albashi na kaso 25/35 ya ce yanzu haka maganar tana kan teburin gwamna Dikko Umar Raɗɗa jira ake akwai ya bada umarni.

Ya ƙara da cewa maganar ƙarin albashi da ƙungiyar ƙwadago ya bijiro da shi, ya tsayar da batun, amma tuni an gama wannan maganar, yana mai cewa ya sanar da duk manyan makarantun da suke ƙarƙashin kulawar ma’aikatarsa, inda aka kwana da inda aka tashi akan batun ƙarin albashi, amma ba wai an fasa ba.

Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya ce akwai abubuwa da yawa da gwamnatin jihar Katsina ta shirya yi ɓangaren ilimi wanda ya ce wasu ba zai faɗe su ba yanzu, sai nan gaba saboda mahimmancin su ga jihar Katsina.

Ya kuma ƙalubalanci jami’ar Yar’adua wanda ya ce gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya yi alkawarin cewa duk dalibin da ya fita da digiri mai daraja ta farko zai ɗauke aiki ba tare da ɓata lokaci ba, amma ya ce kusan wata biyu da yin wannan batu har gobe jami’ar bata rubutu a rubuce ba tana san a aiwatar da wancan alƙawari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUIlimiKatsinaStrikeUniversityYakin aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana’antar Kera Bayanan Kayayyakin Laturoni Ta Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Bunkasuwa Daga Janairu Zuwa Mayu

Next Post

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

Related

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

5 days ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

6 days ago
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50
Ilimi

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

6 days ago
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano
Ilimi

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

1 week ago
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya
Ilimi

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

1 week ago
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano
Ilimi

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

1 week ago
Next Post
Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

July 24, 2025
Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

July 24, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

July 24, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

July 24, 2025
Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

July 24, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

July 24, 2025
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

July 24, 2025
Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

July 24, 2025
Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

July 24, 2025
Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

July 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.