• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Riƙa Bincike Kafin Ku Yi Magana, Martanin Gwamnatin Katsina Ga ASUU

by El-Zaharadeen Umar
11 months ago
in Ilimi
0
Ku Riƙa Bincike Kafin Ku Yi Magana, Martanin Gwamnatin Katsina Ga ASUU
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Katsina ta mayar wa ƙungiyar Malaman jami’a ASUU reshen jami’ar Yar’adua da ke Katsina martani dangane da iƙirarin da ƙungiyar ta yi na cewa jami’ar ta kama hanyar durƙushewa. 

Kwamishinan ma’aikatan ilimi mai zurfi da kula da ƙere-ƙere Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya maida martanin ne da cewa ba gwamnatin su ba ce ta rage kuɗaɗen gudanarwar jami’ar ba.

“Wannan gwamnatin ƙarkashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa bata taɓa rage ko Naira ba daga kuɗaɗen gudanarwa da ake ba jami’ar Yar’adua kuma ba a taɓa fashin biyan su ba.”inji shi.

Kwamishinan wanda ya ce shi daya ne daga cikin Malaman jami’ar kafin ya samu muƙami yasan duk abinda ke faruwa yana da masaniyar musamman tafiyar da sha’anin jami’ar

  • ASUU Ta Bada Wa’adin Mako 3 Ga Gwamnatin Tarayya, Ta Yi Barazanar Shiga Sabon Yajin aiki
  • Jami’ar Yar’adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa – ASUU

Kazalika ya yi kira ga ƙungiyar ASUU da ta koma jami’ar ta bincika ta gani daga yaushe ne aka rage waɗancan kuɗaɗen da suke magana, ba wai su fito a kafafen yaɗa labarai suna faɗin abinda ba haka yake ba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

Sannan ya ƙara da cewa babu wanda ya taɓa rubutawa gwamnati cewa kuɗaɗen gudanarwa da ake ba jami’ar da sauran manyan makarantu ba sa isar su, babu wanda ya taɓa sanar da gwamnati.

“Kuma ina san jama’a da su gane, ASUU sun ce adadin ɗalibai da tsangaya sun ƙaro, to su bayyanawa duniya adadin kuɗaɗen shiga da suke samu a yanzu kowa ya sani.

A cewar sa, ko Naira ɗaya basa ba gwamnatin jihar Katsina, su ke tara kuɗin su, su ke kashe su, saboda haka ya ce su je su bincika tun shekarar 2015 aka fara zabtare kuɗaɗen gudanarwa na jami’ar da sauran makarantu guda biyar.

Da kwamishinan ya juya game da korafin da ƙungiyar ASUU ta yi na cewa gwamnatin tarayya ta fara aiwatar da shirin ƙarin albashi na kaso 25/35 ya ce yanzu haka maganar tana kan teburin gwamna Dikko Umar Raɗɗa jira ake akwai ya bada umarni.

Ya ƙara da cewa maganar ƙarin albashi da ƙungiyar ƙwadago ya bijiro da shi, ya tsayar da batun, amma tuni an gama wannan maganar, yana mai cewa ya sanar da duk manyan makarantun da suke ƙarƙashin kulawar ma’aikatarsa, inda aka kwana da inda aka tashi akan batun ƙarin albashi, amma ba wai an fasa ba.

Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya ce akwai abubuwa da yawa da gwamnatin jihar Katsina ta shirya yi ɓangaren ilimi wanda ya ce wasu ba zai faɗe su ba yanzu, sai nan gaba saboda mahimmancin su ga jihar Katsina.

Ya kuma ƙalubalanci jami’ar Yar’adua wanda ya ce gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya yi alkawarin cewa duk dalibin da ya fita da digiri mai daraja ta farko zai ɗauke aiki ba tare da ɓata lokaci ba, amma ya ce kusan wata biyu da yin wannan batu har gobe jami’ar bata rubutu a rubuce ba tana san a aiwatar da wancan alƙawari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUIlimiKatsinaStrikeUniversityYakin aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana’antar Kera Bayanan Kayayyakin Laturoni Ta Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Bunkasuwa Daga Janairu Zuwa Mayu

Next Post

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

6 days ago
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Ilimi

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

7 days ago
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
Ilimi

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

7 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

1 week ago
Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu
Ilimi

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

2 weeks ago
Next Post
Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Katsina

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.