ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Riƙa Bincike Kafin Ku Yi Magana, Martanin Gwamnatin Katsina Ga ASUU

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta mayar wa ƙungiyar Malaman jami’a ASUU reshen jami’ar Yar’adua da ke Katsina martani dangane da iƙirarin da ƙungiyar ta yi na cewa jami’ar ta kama hanyar durƙushewa. 

Kwamishinan ma’aikatan ilimi mai zurfi da kula da ƙere-ƙere Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya maida martanin ne da cewa ba gwamnatin su ba ce ta rage kuɗaɗen gudanarwar jami’ar ba.

“Wannan gwamnatin ƙarkashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa bata taɓa rage ko Naira ba daga kuɗaɗen gudanarwa da ake ba jami’ar Yar’adua kuma ba a taɓa fashin biyan su ba.”inji shi.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan wanda ya ce shi daya ne daga cikin Malaman jami’ar kafin ya samu muƙami yasan duk abinda ke faruwa yana da masaniyar musamman tafiyar da sha’anin jami’ar

  • ASUU Ta Bada Wa’adin Mako 3 Ga Gwamnatin Tarayya, Ta Yi Barazanar Shiga Sabon Yajin aiki
  • Jami’ar Yar’adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa – ASUU

Kazalika ya yi kira ga ƙungiyar ASUU da ta koma jami’ar ta bincika ta gani daga yaushe ne aka rage waɗancan kuɗaɗen da suke magana, ba wai su fito a kafafen yaɗa labarai suna faɗin abinda ba haka yake ba.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Sannan ya ƙara da cewa babu wanda ya taɓa rubutawa gwamnati cewa kuɗaɗen gudanarwa da ake ba jami’ar da sauran manyan makarantu ba sa isar su, babu wanda ya taɓa sanar da gwamnati.

“Kuma ina san jama’a da su gane, ASUU sun ce adadin ɗalibai da tsangaya sun ƙaro, to su bayyanawa duniya adadin kuɗaɗen shiga da suke samu a yanzu kowa ya sani.

A cewar sa, ko Naira ɗaya basa ba gwamnatin jihar Katsina, su ke tara kuɗin su, su ke kashe su, saboda haka ya ce su je su bincika tun shekarar 2015 aka fara zabtare kuɗaɗen gudanarwa na jami’ar da sauran makarantu guda biyar.

Da kwamishinan ya juya game da korafin da ƙungiyar ASUU ta yi na cewa gwamnatin tarayya ta fara aiwatar da shirin ƙarin albashi na kaso 25/35 ya ce yanzu haka maganar tana kan teburin gwamna Dikko Umar Raɗɗa jira ake akwai ya bada umarni.

Ya ƙara da cewa maganar ƙarin albashi da ƙungiyar ƙwadago ya bijiro da shi, ya tsayar da batun, amma tuni an gama wannan maganar, yana mai cewa ya sanar da duk manyan makarantun da suke ƙarƙashin kulawar ma’aikatarsa, inda aka kwana da inda aka tashi akan batun ƙarin albashi, amma ba wai an fasa ba.

Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya ce akwai abubuwa da yawa da gwamnatin jihar Katsina ta shirya yi ɓangaren ilimi wanda ya ce wasu ba zai faɗe su ba yanzu, sai nan gaba saboda mahimmancin su ga jihar Katsina.

Ya kuma ƙalubalanci jami’ar Yar’adua wanda ya ce gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya yi alkawarin cewa duk dalibin da ya fita da digiri mai daraja ta farko zai ɗauke aiki ba tare da ɓata lokaci ba, amma ya ce kusan wata biyu da yin wannan batu har gobe jami’ar bata rubutu a rubuce ba tana san a aiwatar da wancan alƙawari.

Katsina
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yusuf Buhari Ya Halarci Zaɓen Fidda Gwani Na Sanatan Shiyyar Daura
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mace Ta Doke Namiji A Zaɓen Fidda Gwani Na Majalisar Tarayya A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Gayyato Jakadun Kasashen Waje 17 Ya Kara Wa Bukukuwan Sallah Armashi A Katsina

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Yi Jigila Cikin Sauri A Farkon Watanni 6 Da Suka Gabata Ya Zarce Biliyan 80

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.