• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lamunin Naira Biliyan 5 Ga ‘Yan Fim: Yaushe Kannywood Za Ta Samu Nata?

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
12 months ago
in Nishadi
0
kannywood
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A tsakiyar makon da ya gabata ne aka samu labarin cewa gwamnatin tarayya ta bayar da karin wani kaso daga tallafin naira biliyan 5 ga masana’antar Nollywood, wanda labarin ya karade kafofin yada labarai a kasar nan.

Gwamnatin tarayyar ta ce wannan shi ne rukuni na biyu da ta bayar da irin wannan tallafi ga masana’antar Nollywood da ke shirya fina-finai da harshen Turanci a Nijeriya.

  • Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma
  • Ma’aikatan Ruwa Na Jihar Kaduna Sun Yi Zanga-zangar Rashin Albashi

Gwamnatin tarayya tare da hadin gwiwar bankin Probidus sun bayar da kaso na biyu na kudaden da aka ware domin bunkasa harkokin masana’antun nishadi a Nijeriya, wanda kudin ya kai naira biliyan 5. An kafa wannan asusu ne a watan Disambar 2023, domin tallafawa da kuma bunkasa fannin kirkire-kirkire a Nijeriya.

Mataimaki na musamman ga ofishin mataimakin shugaban kasa kan fasahar tattalin arzikin zamani, Fegho Umunubo, ya sanar da labarin a cikin wani sakonsa a kafar sada zumanta ta ‘Instagram’ da ya wallafa.
Ya ce karkashin sabon tsarin sabunta fata na Shugaba kasa, Bola Ahmed Tinubu, “Mun yi nasarar kaddamar da kashi na biyu na susun tallafa wa masana’antar kirkire-kirkire ta Nijeriya da naira biliyan 5 tare da hadin gwiwar bankin Probidus da kuma otel din Eko Hotels and Suites a ranar Juma’ar da ta gabata.

“Bayan nasarar raba naira biliyan 1.5 ga ’yan wasa hudu da masu shirya fina-finai a masana’antar Nollywood, har yanzu kofa a bude take ga duk masu bukatar tallafi domin bunkasa harkokinsu na nishadi da kirkire-kirkire,” ya rubuta.

Labarai Masu Nasaba

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

A watan Mayu na wannan shekarar aka raba kason farko na naira biliyan 1.5 ga jarumai da masu shirya fina-finai hudu.

Sai dai Fegho ya ce kudaden ba kyauta ba ne, domin ana sa ran wadanda suka amfana za su mayar da kashi 30 cikin 100 na kudaden da suka samu zuwa bankin Probidus a dan kankanin lokaci.

Hakan ya sa mutane da dama suke sha’awar ganin takwarar masana’antar Nollywood, wadda take shirya fina-finanta da harshen Hausa wato Kannywood ita ma ta samu kwatankwacin irin wannan tallafin, duba da cewa a lokuta da dama kamar dai Nollywood ita ma masana’antar Kannywood takan rasa wasu kudaden da za ta gudanar da wani abu wanda zai janyo mata ci gaba ya kuma daukaka sunan Nijeriya a idon duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ali NuhuKannywoodNishadi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Shugaban Sin Ya Yi Jawabi A Dandalin Tattaunawar Zaman Lafiyar Duniya Karo Na 12

Next Post

Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

Related

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

10 hours ago
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

1 week ago
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba
Nishadi

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

3 weeks ago
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

4 weeks ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

1 month ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

1 month ago
Next Post
Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

LABARAI MASU NASABA

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.