• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Kano sun bayyana cewa a kasar da babu manufa ce kadai, jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso zai iya zama shugaban kasa. Sun kara da cewa NNPP za ta sha wahala wajen sake neman a zabenta a Jihar Kano a 2027 ba kamar yadda suke ikirarin cewa, Shugaban kasa Bola Tinubu ne zai wahala ba.

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas, ya bayyana cewa a yanzu haka jam’iyyarsu ta kara samun hadin kai tare da dinke barakar da suka samu a zaben da ya gabata kuma sun shirya tsaf wajen kayar da NNPP a Jihar Kano.

  • Jagororin Siyasar Arewa Raunana Ne Kuma A Rarrabe Suke – Salihu Lukman
  • Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

Jigon APC ya ce sabanin rahoton da kafafen yada labarai suka bayar ga shugaban NNPP na Jihar Kano, Hashimu Dungurawa, jam’iyyar da ke mulkin jihar da jagoranta na kasa, Rabi’u Musa Kwankwaso ne za su fuskanci mummunar matsala kan rikicin masarautar Jihar Kano.

Shugaban jam’iyyar NNPP na Kano ya ce rikicin sarautar Jihar Kano na iya yin illa ga burin Shugaba Bola Tinubu wajen ci gba da mulki a karo na biyu a 2027.

Sai dai a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano ya ce ikirarin da shugaban jam’iyyar NNPP, Dungurawa ya yi alama ce da ke nuna gazawar jam’iyyar a jihar da kuma kasa baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Abbas ya kara da cewa abun kunya ne ya bayyana haka ganin irin rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar NNPP da kuma jagoranta, Kwankwaso, abin kunya ne ya yi ikirarin sake lashe zabe a 2027.

“An ce Kwankwaso ya samu kuri’u 1,454,649 a zaben 2023, wanda ke wakiltar kashi 6.23 ne kawai, kuma yawancinsu daga Kano ne ya samu kuri’un. Amma binciken da kafafen yada labarai suka yi bayan zaben ya nuna cewa Kwankwaso bai samu kuri’u 100,000 a wata jiha ban da Kano.”

Abbas ya yi nuni da cewa Kwankwaso ya samu kuri’u miliyan 1.2 ko kashi 19 cikin 100 na kuri’un da aka kada a yankin arewa maso yamma a yankinsa, kuma kusan bai samu komai ba a sauran yankunan kasar nan.

“Ta yaya za a yi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi daga kudu maso gabas ya yi wa Kwankwaso fintinkau a jihohi 13 na arewa kamar Kaduna, Taraba, Borno, Gombe, Kebbi, Kogi, Kwara, Neja, Sakkwato, Nasarawa, Filato, Adamawa da kuma Benuwai,” in ji shi.

Shugaban jam’iyyar APC ya ce al’ummar Kano da masu tunani a arewacin Nijeriya sun fahimci cewa, abin da gwamnatin tarayya ke bukata a rikicin masarautar Kano shi ne, ta tabbatar da doka da oda domin a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin al’umma jihar.

A cewarsa, a zaben 2027, al’ummar Jihar Kano wadanda aka rusa gidajensu ba za su manta ba, al’ummar Jihar Kano wadanda aka lalata musu hanyoyin samun tattalin arziki da kasuwanci ba za su sake zaben NNPP ba. Mutanen da dama gwamnatin Jihar Kano ta daidaita.

Shugaban APC na Jihar Kano ya bayyana cewa batun zaben shugaban kasa a 2027 da shugaban jam’iyyar NNPP na Kano ya yi barazanar za su kayar da su a Kano manuniya ce ga gazawar gwamnatinsu, sannan kuma za su yi amfani da dukiyar al’ummar Jihar Kano wajen tallata Kwankwaso wanda ba zai iya zama shugaban kasa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGwamnatin GandujeKwankwasiyyaNNPP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manoma Na Bukatar A Yi Rangwamen Kayan Aikin Noma – Wasu Jami’ai

Next Post

Kamfanin Sin Ya Fara Gina Hanyar Motoci Masu Saurin Tafiya Ta Farko A Cote Di’voire

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

2 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

4 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Kamfanin Sin Ya Fara Gina Hanyar Motoci Masu Saurin Tafiya Ta Farko A Cote Di’voire

Kamfanin Sin Ya Fara Gina Hanyar Motoci Masu Saurin Tafiya Ta Farko A Cote Di’voire

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.