ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kwankwaso

Shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Kano sun bayyana cewa a kasar da babu manufa ce kadai, jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso zai iya zama shugaban kasa. Sun kara da cewa NNPP za ta sha wahala wajen sake neman a zabenta a Jihar Kano a 2027 ba kamar yadda suke ikirarin cewa, Shugaban kasa Bola Tinubu ne zai wahala ba.

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas, ya bayyana cewa a yanzu haka jam’iyyarsu ta kara samun hadin kai tare da dinke barakar da suka samu a zaben da ya gabata kuma sun shirya tsaf wajen kayar da NNPP a Jihar Kano.

  • Jagororin Siyasar Arewa Raunana Ne Kuma A Rarrabe Suke – Salihu Lukman
  • Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

Jigon APC ya ce sabanin rahoton da kafafen yada labarai suka bayar ga shugaban NNPP na Jihar Kano, Hashimu Dungurawa, jam’iyyar da ke mulkin jihar da jagoranta na kasa, Rabi’u Musa Kwankwaso ne za su fuskanci mummunar matsala kan rikicin masarautar Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Shugaban jam’iyyar NNPP na Kano ya ce rikicin sarautar Jihar Kano na iya yin illa ga burin Shugaba Bola Tinubu wajen ci gba da mulki a karo na biyu a 2027.

Sai dai a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano ya ce ikirarin da shugaban jam’iyyar NNPP, Dungurawa ya yi alama ce da ke nuna gazawar jam’iyyar a jihar da kuma kasa baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Abbas ya kara da cewa abun kunya ne ya bayyana haka ganin irin rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar NNPP da kuma jagoranta, Kwankwaso, abin kunya ne ya yi ikirarin sake lashe zabe a 2027.

“An ce Kwankwaso ya samu kuri’u 1,454,649 a zaben 2023, wanda ke wakiltar kashi 6.23 ne kawai, kuma yawancinsu daga Kano ne ya samu kuri’un. Amma binciken da kafafen yada labarai suka yi bayan zaben ya nuna cewa Kwankwaso bai samu kuri’u 100,000 a wata jiha ban da Kano.”

Abbas ya yi nuni da cewa Kwankwaso ya samu kuri’u miliyan 1.2 ko kashi 19 cikin 100 na kuri’un da aka kada a yankin arewa maso yamma a yankinsa, kuma kusan bai samu komai ba a sauran yankunan kasar nan.

“Ta yaya za a yi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi daga kudu maso gabas ya yi wa Kwankwaso fintinkau a jihohi 13 na arewa kamar Kaduna, Taraba, Borno, Gombe, Kebbi, Kogi, Kwara, Neja, Sakkwato, Nasarawa, Filato, Adamawa da kuma Benuwai,” in ji shi.

Shugaban jam’iyyar APC ya ce al’ummar Kano da masu tunani a arewacin Nijeriya sun fahimci cewa, abin da gwamnatin tarayya ke bukata a rikicin masarautar Kano shi ne, ta tabbatar da doka da oda domin a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin al’umma jihar.

A cewarsa, a zaben 2027, al’ummar Jihar Kano wadanda aka rusa gidajensu ba za su manta ba, al’ummar Jihar Kano wadanda aka lalata musu hanyoyin samun tattalin arziki da kasuwanci ba za su sake zaben NNPP ba. Mutanen da dama gwamnatin Jihar Kano ta daidaita.

Shugaban APC na Jihar Kano ya bayyana cewa batun zaben shugaban kasa a 2027 da shugaban jam’iyyar NNPP na Kano ya yi barazanar za su kayar da su a Kano manuniya ce ga gazawar gwamnatinsu, sannan kuma za su yi amfani da dukiyar al’ummar Jihar Kano wajen tallata Kwankwaso wanda ba zai iya zama shugaban kasa ba.

Kwankwaso
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Kamfanin Sin Ya Fara Gina Hanyar Motoci Masu Saurin Tafiya Ta Farko A Cote Di’voire

Kamfanin Sin Ya Fara Gina Hanyar Motoci Masu Saurin Tafiya Ta Farko A Cote Di’voire

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.