ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kwankwaso

Shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Kano sun bayyana cewa a kasar da babu manufa ce kadai, jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso zai iya zama shugaban kasa. Sun kara da cewa NNPP za ta sha wahala wajen sake neman a zabenta a Jihar Kano a 2027 ba kamar yadda suke ikirarin cewa, Shugaban kasa Bola Tinubu ne zai wahala ba.

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas, ya bayyana cewa a yanzu haka jam’iyyarsu ta kara samun hadin kai tare da dinke barakar da suka samu a zaben da ya gabata kuma sun shirya tsaf wajen kayar da NNPP a Jihar Kano.

  • Jagororin Siyasar Arewa Raunana Ne Kuma A Rarrabe Suke – Salihu Lukman
  • Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

Jigon APC ya ce sabanin rahoton da kafafen yada labarai suka bayar ga shugaban NNPP na Jihar Kano, Hashimu Dungurawa, jam’iyyar da ke mulkin jihar da jagoranta na kasa, Rabi’u Musa Kwankwaso ne za su fuskanci mummunar matsala kan rikicin masarautar Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Shugaban jam’iyyar NNPP na Kano ya ce rikicin sarautar Jihar Kano na iya yin illa ga burin Shugaba Bola Tinubu wajen ci gba da mulki a karo na biyu a 2027.

Sai dai a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano ya ce ikirarin da shugaban jam’iyyar NNPP, Dungurawa ya yi alama ce da ke nuna gazawar jam’iyyar a jihar da kuma kasa baki daya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Abbas ya kara da cewa abun kunya ne ya bayyana haka ganin irin rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar NNPP da kuma jagoranta, Kwankwaso, abin kunya ne ya yi ikirarin sake lashe zabe a 2027.

“An ce Kwankwaso ya samu kuri’u 1,454,649 a zaben 2023, wanda ke wakiltar kashi 6.23 ne kawai, kuma yawancinsu daga Kano ne ya samu kuri’un. Amma binciken da kafafen yada labarai suka yi bayan zaben ya nuna cewa Kwankwaso bai samu kuri’u 100,000 a wata jiha ban da Kano.”

Abbas ya yi nuni da cewa Kwankwaso ya samu kuri’u miliyan 1.2 ko kashi 19 cikin 100 na kuri’un da aka kada a yankin arewa maso yamma a yankinsa, kuma kusan bai samu komai ba a sauran yankunan kasar nan.

“Ta yaya za a yi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi daga kudu maso gabas ya yi wa Kwankwaso fintinkau a jihohi 13 na arewa kamar Kaduna, Taraba, Borno, Gombe, Kebbi, Kogi, Kwara, Neja, Sakkwato, Nasarawa, Filato, Adamawa da kuma Benuwai,” in ji shi.

Shugaban jam’iyyar APC ya ce al’ummar Kano da masu tunani a arewacin Nijeriya sun fahimci cewa, abin da gwamnatin tarayya ke bukata a rikicin masarautar Kano shi ne, ta tabbatar da doka da oda domin a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin al’umma jihar.

A cewarsa, a zaben 2027, al’ummar Jihar Kano wadanda aka rusa gidajensu ba za su manta ba, al’ummar Jihar Kano wadanda aka lalata musu hanyoyin samun tattalin arziki da kasuwanci ba za su sake zaben NNPP ba. Mutanen da dama gwamnatin Jihar Kano ta daidaita.

Shugaban APC na Jihar Kano ya bayyana cewa batun zaben shugaban kasa a 2027 da shugaban jam’iyyar NNPP na Kano ya yi barazanar za su kayar da su a Kano manuniya ce ga gazawar gwamnatinsu, sannan kuma za su yi amfani da dukiyar al’ummar Jihar Kano wajen tallata Kwankwaso wanda ba zai iya zama shugaban kasa ba.

Kwankwaso
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Kwankwaso
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Kamfanin Sin Ya Fara Gina Hanyar Motoci Masu Saurin Tafiya Ta Farko A Cote Di’voire

Kamfanin Sin Ya Fara Gina Hanyar Motoci Masu Saurin Tafiya Ta Farko A Cote Di’voire

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.