• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ita Kadai Ba Za Ta Iya Daukar Dawainiyar Kudaden Ilimi Ba – Minista

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
ilimi

Ministan ilimi, Farfesa Tahir Mamman, ya shaida cewar gwamnatin tarayya ita kadai ba za ta iya daukan dawainiyar kudaden da sashin ilimi ke bukata a Nijeriya ba.

Ya shaida hakan ne a Abuja a yayin wani taro da aka shirya domin karrama Dakta Emeka Offor da matarsa, Dakta Adaora Offor wadanda suka samu lambar yabon digiri ta karramawa a bangaren tafiyar da harkokin kasuwanci da kuma shawarorin zamantakewa wanda jami’ar Nigeria Nsukka (UNN) da jami’ar Nnamdi Azikiwe (NAU), Awka suka ba su.

  • Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Fityanul Islam Ta Zaburar Da Musulmi Kan Bin Addini

Ministan ya ce gwamnati na kashe maguden kudade wajen daukan nauyin ilimi, don haka akwai bukatar daidaikun mutane da masu hannu da shuni da su kwaikwayi abun da Mista Offor da matarsa suka yi ta hanyar gidauniyarsu na taimakon ilimi.

Ya ce, “Ma’aikatarmu tana karfafan irin wannan karamcin, saboda gwamnati ba za ta iya dauke dawainiyar kudaden ilimi ita kadai ba, domin tana ba da gudunma-wa sosai.

“Wannan dalilin ne ya sanya mutane irin su Emeka Offor da matarsa suka shigo cikin lamarin, sannan akwai bukatar a karfafa musu guiwa. Na yi amanar wannan shi ne irin misalin kashe kudade ta hanyoyin da suka dace, don haka, ina kira ga sauran masu hannu da shuni da su yi koyi da abun da su din suka yi.”

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Yayin da jami’ar UNN ta amshi naira miliyan 100 domin harkokin da suka shafi zurfafa bincike da nazarin ilimi tare da masana harkokin kasuwanci domin ingant-awa da tabbatar da yin tasiri a tsangayar koyar da ilimin harkokin gudanar da kasuwanci, inda ita kuma jami’ar NAU ta amshi naira miliyan 50 a matsayin tal-lafin kula da walwalar zawarawa, yara da suke fama da bukata ta musamman da kuma sauran jama’a da ke cikin yanayi na fatara.

Mai ba da tallafin, Cif Offor ya ce, wannan tallafin ba shi ne na karshe ba, kuma za su ci gaba da yin duk mai yiyuwa domin taimaka wa jami’o’in Nijeriya.

Ya ce, “Wannan tallafin na daga cikin manufarmu na ganin mun taimaka wa ilimi a manyan matakai a Nijeriya,” sai ya nemi karin hadin guiwa a tsakanin gidauniyar-sa ta SEOF da kuma jami’o’in UNN da NAU.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
Foamy Urine

Matsalar Da Ke Haifar Da Fitsari Mai Kumfa (Foamy Urine)

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.