ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
ilimi

Wani masani kuma kwararre a fannin koyo da koyarwa, sannan kuma hamshakin marubuci, Michael Omisore ya bayyana nasa dalilin na rashin samun malamai a wannan fanni na manayan darussa biyu; lissafi da kuma turanci, inda ya ce; hakan yana nuni da irin rikon sakainar kashin da ake yi wa aikin koyarwa a tsakanin al’umma.

“Darussan da dole ne sai dalibai sun samu nasara akansu, me zai sa ba za mu dauki malaman darussan, don cike wannan gurbi ba?”.

Ya ce, “Ina yin hulda da daruruwan masu nakarantu nasu na kansu a fadin tarayyar Nijeriya, wasu daga cikinsu na tambaya ta ko zan sama masu malaman Turanci gwanaye wadanda za su dauka aiki, wadansu ma har wajen zama za su ba wa malaman suka dauka.

ADVERTISEMENT

“Don haka, me yasa ba ma daukar kwararru wadanda suke neman wannan aiki, tunda muna da wadanda suke da satifiket na kammala karatun NCE masu neman aikin yi, musamman wadabda suka karanta wadannan darussa na LIssafi da Turanci ko darussan da suke da alaka da su?”.

“Ko shakka babu, ana iya gano wadannan dalilai ta bangarori uku; yadda aka nuna lamarin ilimi a halin yanzu ba shi da wani muhimmanci, dole ne mu yi watsi da hakan, idan har ana so a dawo da martabar aikin koyarwa,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Albashin Malaman Makarantu
Kamar yadda Hausawa ke cewa, ladan malamin makaranta sai a lahira zai same shi, wannan lamari ko kadan ba haka yake ba. Dalili kuwa, ko me aka bai wa malamin makaranta; ba a biya shi ba, don kuwa ya dace a tuna da cewa shi ma yana da matsalolin da suke bukatar magani.

Kamar yadda aka sani ne cewa, babban aikin malamin makaranta shi ne koyarwa, amma albashinsa bai taka kara ya karya ba, duk da cewa abin ba a kan malamin makarantar kadai ya tsaya ba; sannan akwai wadansu abubuwa masu amfani, amma mutane na nuna kamar ba su san amfanin nasa ba.

Abin da marubucin wannan makala ke kallo shi ne, idan ana maganar albashi, shi ne abin da ya kamata ma’aikaci ya yi tinkaho da shi.

Misali, da zarar an dauki ma’aikaci aiki; a matsayinsa na malamin Turanci; a kan yi alkawari za a rika ba shi albashin Naira 50,000 a kowane wata, wannan shi ne abin da zai rika sa ran gani matsayin albashi kowane wata.

Idan ya fara aikin shekara daya zuwa biyu aka kuma samun kari, za a yi tsammanin samun karin wannan albashi, idan kuma ba a samu ba sai abubuwa su fara canzawa, musamman idan mai makarantar ya ki yin karin albashin da ya kamata ya yi, malamin na iya zuwa wani wuri daban neman wani aikin koyarwar ga kuma kwarewar da ya samu ta aiki a wannan wurin.

Saboda haka, idan ya samu wata makarantar ana iya biyan sa kimanin Naira 75,000, ko kuma albashin ya zarce na wancan makarantar da ya bari. Malaman Turanci da na Lissafi, ana matukar bukatar su idan kuma har aka dace sun san darussan sosai, suna iya samun aiki a kowane lokaci tare da albashi mai tsoka lokaci zuwa lokaci.

Omisore ya kara da cewa, a nasa ganin abu na biyu bayan wannan albashi shi ne, yadda su malaman suka dauki lamarin koyarwa a matsayin aiki ne kawai; ba abin da suka karanta a makaranta domin su rayu da shi. A cewar tasa, wannan lamari na matukar damun sa idan ya ga malamai suna neman hada kansu da Injiniyoyi ko Akantoci ko kuma Lauyoyi, duk da cewa fa su ne suka zaba wa kansu wannan fanni da suka karanta, amma kuwa sun buge da hange-hange wasu daban.

Wasu malaman na yi wa wannan lamari na koyarwa kallon albashi ne kadai, ba sa kallon albarkar da ke cikin aikin na koyarwa da kuma irin kwarewar da suke samu a kan aikin, wanda ta hakan kuma wata damar daban za ta iya samuwa.

ilimi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
ilimi
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

MASU ALAKA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Next Post
kotu

Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.