ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
ilimi

Wani masani kuma kwararre a fannin koyo da koyarwa, sannan kuma hamshakin marubuci, Michael Omisore ya bayyana nasa dalilin na rashin samun malamai a wannan fanni na manayan darussa biyu; lissafi da kuma turanci, inda ya ce; hakan yana nuni da irin rikon sakainar kashin da ake yi wa aikin koyarwa a tsakanin al’umma.

“Darussan da dole ne sai dalibai sun samu nasara akansu, me zai sa ba za mu dauki malaman darussan, don cike wannan gurbi ba?”.

Ya ce, “Ina yin hulda da daruruwan masu nakarantu nasu na kansu a fadin tarayyar Nijeriya, wasu daga cikinsu na tambaya ta ko zan sama masu malaman Turanci gwanaye wadanda za su dauka aiki, wadansu ma har wajen zama za su ba wa malaman suka dauka.

ADVERTISEMENT

“Don haka, me yasa ba ma daukar kwararru wadanda suke neman wannan aiki, tunda muna da wadanda suke da satifiket na kammala karatun NCE masu neman aikin yi, musamman wadabda suka karanta wadannan darussa na LIssafi da Turanci ko darussan da suke da alaka da su?”.

“Ko shakka babu, ana iya gano wadannan dalilai ta bangarori uku; yadda aka nuna lamarin ilimi a halin yanzu ba shi da wani muhimmanci, dole ne mu yi watsi da hakan, idan har ana so a dawo da martabar aikin koyarwa,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Albashin Malaman Makarantu
Kamar yadda Hausawa ke cewa, ladan malamin makaranta sai a lahira zai same shi, wannan lamari ko kadan ba haka yake ba. Dalili kuwa, ko me aka bai wa malamin makaranta; ba a biya shi ba, don kuwa ya dace a tuna da cewa shi ma yana da matsalolin da suke bukatar magani.

Kamar yadda aka sani ne cewa, babban aikin malamin makaranta shi ne koyarwa, amma albashinsa bai taka kara ya karya ba, duk da cewa abin ba a kan malamin makarantar kadai ya tsaya ba; sannan akwai wadansu abubuwa masu amfani, amma mutane na nuna kamar ba su san amfanin nasa ba.

Abin da marubucin wannan makala ke kallo shi ne, idan ana maganar albashi, shi ne abin da ya kamata ma’aikaci ya yi tinkaho da shi.

Misali, da zarar an dauki ma’aikaci aiki; a matsayinsa na malamin Turanci; a kan yi alkawari za a rika ba shi albashin Naira 50,000 a kowane wata, wannan shi ne abin da zai rika sa ran gani matsayin albashi kowane wata.

Idan ya fara aikin shekara daya zuwa biyu aka kuma samun kari, za a yi tsammanin samun karin wannan albashi, idan kuma ba a samu ba sai abubuwa su fara canzawa, musamman idan mai makarantar ya ki yin karin albashin da ya kamata ya yi, malamin na iya zuwa wani wuri daban neman wani aikin koyarwar ga kuma kwarewar da ya samu ta aiki a wannan wurin.

Saboda haka, idan ya samu wata makarantar ana iya biyan sa kimanin Naira 75,000, ko kuma albashin ya zarce na wancan makarantar da ya bari. Malaman Turanci da na Lissafi, ana matukar bukatar su idan kuma har aka dace sun san darussan sosai, suna iya samun aiki a kowane lokaci tare da albashi mai tsoka lokaci zuwa lokaci.

Omisore ya kara da cewa, a nasa ganin abu na biyu bayan wannan albashi shi ne, yadda su malaman suka dauki lamarin koyarwa a matsayin aiki ne kawai; ba abin da suka karanta a makaranta domin su rayu da shi. A cewar tasa, wannan lamari na matukar damun sa idan ya ga malamai suna neman hada kansu da Injiniyoyi ko Akantoci ko kuma Lauyoyi, duk da cewa fa su ne suka zaba wa kansu wannan fanni da suka karanta, amma kuwa sun buge da hange-hange wasu daban.

Wasu malaman na yi wa wannan lamari na koyarwa kallon albashi ne kadai, ba sa kallon albarkar da ke cikin aikin na koyarwa da kuma irin kwarewar da suke samu a kan aikin, wanda ta hakan kuma wata damar daban za ta iya samuwa.

ilimi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • Sulaiman
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa
ilimi
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Jihohi Suka Fara Ɗanɗana Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    ‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

MASU ALAKA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
kotu

Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.