• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CAF 2025: Nijeriya Ta Fito A Rukuni Mai Zafi

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Wasanni
0
caf 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya ta fito a cikin rukuni mai wahala a jada-walin wasannin neman cancantar shiga gasar cin kofin Afirka na shekara ta 2025 da za a buga a kasar Morocco.

Sai dai da alama mai kare kambun gasar Nahiyar Afrika, wato Ibory Coast, za ta iya kaiwa ga gasar ta 2025 da za a yi a Morocco, amma da alama Nijeriya ta fada wani rukuni mai matukar rintsi da wahala.

Raba rukunin da aka yi a Birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, tawagar Super Eagles ta tsinci kanta cikin rukuni daya da kasashen Benin da Rwanda da kuma kasar Libya.

Yanzu tsohon kocin Nijeriya Gernot Rohr ne ke horar da Benin, kuma ya doke Nijeriya da ci 2-1 a watan jiya a wasannin share fagen shiga gasar kofin duniya ta shekarar 2026.

Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya yanzu na neman sabon koci biyo bayan ajiye aikin da Finidi George ya yi wanda ya koma Ribers United. Sai dai har yanzu hukumar kwallon kafa ta kasar ba ta tabbatar da tafiyarsa ba a hukumance.

Labarai Masu Nasaba

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Ibory Coast da ta lashe gasar nahiyar karo na uku bayan doke Nijeriya a wasan karshe a watan Fabirairu, za ta fafata da gwarzuwar gasar 2012 Zambia, Sierra Leone da kuma Chadi.

Kocin tawagar Ibory Coast, Emerse Fae ya taimaka wajen raba rukunin da aka yi a Jo-hannesburg kuma ya yi farin ciki da sakamakon inda ya ce sun yi wasa da Zambia a wasan share fagen AFCON na baya, saboda haka sun san tawagarsu sosai da sosai.

Tawagar kasashe 48 din an raba su zuwa rukunai 12 ne zuwa kuma gida hudu, yayin da tawagogi biyu na kowanne rukuni za su samu zuwa Morocco a karshe domin buga gasar.

Masu masaukin baki na da kujerar dindindin a gasar, don haka tawaga daya ake nema a rukunin da suke, wanda ya hada da Gabon, Central African Republic da kuma Leso-tho.

Kamar yadda hukumar kula da gasar cin kofin na Afirka ta tsara, za a yi wasanni shida ne na neman gurbin a watan Satumba da Oktoba da kuma watan Nuwambar wannan shekarar. Za a fara wasan AFCON 2025 a ranar 21 ga watan Disambar shekara mai

zuwa, a kuma yi wasan karshe na gasar a ranar 18 ga watan Janairun shekarar 2026 kamar yadda aka tsara.

Gasar za a buga ta ne lokacin da ake wasannin Firimiyar Ingila na karshen shekara da kuma gasar cin kofin zakarun Turai, sannan wannan ne karon farko da ake buga gasar a watan Nuwamba a tarihi, kuma zai shiga lokacin bikin Kirsimeti da sabuwar shekara.

 

Rukunan samun shiga Afcon 2025

Rukunin A: Tunisia, Madagascar, Comoros, The Gambia.- Rukinin B: Morocco, Ga-bon, Central African Republic, Lesotho.- Rukinin C: Egypt, Cape Berde, Mauritania, Botswana.

Rukinin D: Nigeria, Benin, Libya, Rwanda.- Rukinin E: Algeria, Ekuatorial Guinea, To-go, Liberia.- Rukinin F: Ghana, Angola, Sudan, Nijar.- Rukinin G: Ibory Coast, Zambia, Sierra Leone, Chad.- Rukinin H: DR Congo, Guinea, Tanzania, Ethiopia.- Rukinin I: Mali, Mozambikue, Guinea-Bissau, Eswatini.- Rukinin J: Kamaru, Namibia, Kenya, Zimbabwe.- Rukinin K: South Africa, Uganda, Congo, South Sudan. Rukinin L: Senegal, Burkina Faso, Malawi, Burundi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CAFMoroccoSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokar Fansho Ta Majalisar Dokoki: Dokar Son Kai Ko …?Kanun Labarai

Next Post

Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

Related

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

1 day ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

4 days ago
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Wasanni

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

4 days ago
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

6 days ago
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana
Wasanni

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

6 days ago
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

7 days ago
Next Post
jamus

Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.