ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CAF 2025: Nijeriya Ta Fito A Rukuni Mai Zafi

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
caf 2025

Tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya ta fito a cikin rukuni mai wahala a jada-walin wasannin neman cancantar shiga gasar cin kofin Afirka na shekara ta 2025 da za a buga a kasar Morocco.

Sai dai da alama mai kare kambun gasar Nahiyar Afrika, wato Ibory Coast, za ta iya kaiwa ga gasar ta 2025 da za a yi a Morocco, amma da alama Nijeriya ta fada wani rukuni mai matukar rintsi da wahala.

Raba rukunin da aka yi a Birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, tawagar Super Eagles ta tsinci kanta cikin rukuni daya da kasashen Benin da Rwanda da kuma kasar Libya.

ADVERTISEMENT

Yanzu tsohon kocin Nijeriya Gernot Rohr ne ke horar da Benin, kuma ya doke Nijeriya da ci 2-1 a watan jiya a wasannin share fagen shiga gasar kofin duniya ta shekarar 2026.

Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya yanzu na neman sabon koci biyo bayan ajiye aikin da Finidi George ya yi wanda ya koma Ribers United. Sai dai har yanzu hukumar kwallon kafa ta kasar ba ta tabbatar da tafiyarsa ba a hukumance.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Ibory Coast da ta lashe gasar nahiyar karo na uku bayan doke Nijeriya a wasan karshe a watan Fabirairu, za ta fafata da gwarzuwar gasar 2012 Zambia, Sierra Leone da kuma Chadi.

Kocin tawagar Ibory Coast, Emerse Fae ya taimaka wajen raba rukunin da aka yi a Jo-hannesburg kuma ya yi farin ciki da sakamakon inda ya ce sun yi wasa da Zambia a wasan share fagen AFCON na baya, saboda haka sun san tawagarsu sosai da sosai.

Tawagar kasashe 48 din an raba su zuwa rukunai 12 ne zuwa kuma gida hudu, yayin da tawagogi biyu na kowanne rukuni za su samu zuwa Morocco a karshe domin buga gasar.

Masu masaukin baki na da kujerar dindindin a gasar, don haka tawaga daya ake nema a rukunin da suke, wanda ya hada da Gabon, Central African Republic da kuma Leso-tho.

Kamar yadda hukumar kula da gasar cin kofin na Afirka ta tsara, za a yi wasanni shida ne na neman gurbin a watan Satumba da Oktoba da kuma watan Nuwambar wannan shekarar. Za a fara wasan AFCON 2025 a ranar 21 ga watan Disambar shekara mai

zuwa, a kuma yi wasan karshe na gasar a ranar 18 ga watan Janairun shekarar 2026 kamar yadda aka tsara.

Gasar za a buga ta ne lokacin da ake wasannin Firimiyar Ingila na karshen shekara da kuma gasar cin kofin zakarun Turai, sannan wannan ne karon farko da ake buga gasar a watan Nuwamba a tarihi, kuma zai shiga lokacin bikin Kirsimeti da sabuwar shekara.

 

Rukunan samun shiga Afcon 2025

Rukunin A: Tunisia, Madagascar, Comoros, The Gambia.- Rukinin B: Morocco, Ga-bon, Central African Republic, Lesotho.- Rukinin C: Egypt, Cape Berde, Mauritania, Botswana.

Rukinin D: Nigeria, Benin, Libya, Rwanda.- Rukinin E: Algeria, Ekuatorial Guinea, To-go, Liberia.- Rukinin F: Ghana, Angola, Sudan, Nijar.- Rukinin G: Ibory Coast, Zambia, Sierra Leone, Chad.- Rukinin H: DR Congo, Guinea, Tanzania, Ethiopia.- Rukinin I: Mali, Mozambikue, Guinea-Bissau, Eswatini.- Rukinin J: Kamaru, Namibia, Kenya, Zimbabwe.- Rukinin K: South Africa, Uganda, Congo, South Sudan. Rukinin L: Senegal, Burkina Faso, Malawi, Burundi

CAF 2025
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
CAF 2025
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
jamus

Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.