• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasan Karta Na Joe Biden Game Da Xizang Ya Gaza Tun Kan Ya Fara

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Wasan Karta Na Joe Biden Game Da Xizang Ya Gaza Tun Kan Ya Fara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya sanya hannu a hukumance kan kudurin da zai sa kaimi ga samar da shawarwari kan batun Xizang (wato Tibet) da Sin, a ranar 12 ga watan Yuli, wanda ya nuna cewa, gwamnatin Amurka ba ta taba daukar matsayin cewa Xizang yanki ne na kasar Sin ba tun a zamanin da, da cewa dole ne a warware sabani tsakanin Xizang da kasar Sin ta hanyar lumana bisa dokokin kasa da kasa ta hanyar tattaunawa ba tare da wani sharadi ba. 

Wannan wasan karta fakewa ne da guzuma don a harbi karsana, da kuma tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin. Yankin Xizang mai cin gashin kansa wani bangare ne na kasar Sin tun fil azal, kuma harkokin Xizang lamari ne na cikin gida na kasar Sin, wanda ba ya bukatar tsangwama daga wani bangare daga waje. Binciken kayan tarihi da aka yi a wannan yanki na kudu maso yammacin kasar Sin ya nuna dadadden alaka mai karfi da kusanci tsakaninsa da sauran yankunan kasar Sin, wanda ya tabbatar da hadin kan al’ummar kasar Sin mai mabambantan al’adu.

  • Masana Sun Yi Kira Da A Fadada Musayar Al’adu Da Yawon Shakatawa Tsakanin Sin Da Najeriya
  • Shugaban Kasar Sin Ya Jajantawa Donald Trump

Misali, daga cikin kayayyakin tarihi da aka gano a kabarin Guru Jiamu da ke Ali, a wannan yanki, wanda ya samo asali ne daga daular Han ta Gabas kimanin shekaru 2,000 da suka gabata, akwai wani kayan surfani da ya kwashe sama da shekaru 1,800 da suka gabata wanda aka tsara da zanen tsuntsaye da namomin jeji, yana dauke da harafin Sinanci “wanghou,” ma’ana girma, kuma shi ne kayan tarihi na siliki na farko da aka samu a kan tudun Qinghai-Xizang, wanda ya tabbatar da dogon tarihin mu’amalar kud-da-kud tsakanin yankin da sauran sassa da kabilun kasar.

Kokarin gurbata gaskiya ta hanyar kafa dokokin cikin gida kuma bisa radin kai da kuma musanta tarihin cewa Xizang wani bangare ne na kasar Sin tun a zamanin da, wata dabara ce mai cike da rudani don bata wa kasar Sin mutuncinta. Dole ne Amurka ta mutunta ka’idar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”, ta kuma daina goyon bayan duk wani nau’i na neman “yancin kai na Xizang”, da kuma janye sabuwar dokarta ta tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin. Tabbas wannan yunkurin karkata gaskiya zai gaza, kuma zai fuskanci adawa ba da kasar Sin kawai ba, har ma da daga sauran kasashen duniya. (Mohammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ministan Yaɗa Labarai Ya Karɓi Baƙuncin ‘Yan Jaridar Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

Next Post

Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai

Related

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

12 hours ago
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

13 hours ago
Sabbin Gonakin Da Za A Magance Zaizayewar Kasa A Sin A Karshen Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 Sun Kai Muraba’in Kilomita 340,000
Daga Birnin Sin

Sabbin Gonakin Da Za A Magance Zaizayewar Kasa A Sin A Karshen Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 Sun Kai Muraba’in Kilomita 340,000

14 hours ago
Jami’in MDD: Kayataccen Hutun “Golden Week Plus” Na Kasar Sin Ya Nuna Tasirin Yawon Bude Ido A Duniya 
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Kayataccen Hutun “Golden Week Plus” Na Kasar Sin Ya Nuna Tasirin Yawon Bude Ido A Duniya 

15 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

16 hours ago
Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

1 day ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai

Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

October 3, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.