ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

by Rabi'u Ali Indabawa
8 months ago
Yobe

Hedkwatar ‘Yansandan Jihar Yobe ta kama mutum hudu da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a fadin jihar, bayan wani samame da aka gudanar kan masu aikata laifi.

A cewar sanarwar kakakin ‘yansanda, SP Dungus Abdulkarim, a daren Asabar, wannan kamen na nuna jajircewar rundunar wajen tabbatar da doka da oda.

  • Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
  • Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Sanarwar ta kara da cewa, wannan kokari na daga cikin matakan dabarun da rundunar ta dauka domin kawar da aikata laifuka a jihar.

ADVERTISEMENT

Ta bayyana cewa, “A cikin makon da ya gabata, rundunar ta kama mutum hudu bisa zargin aikata laifuka daban-daban a sassa daban-daban na jihar, baya ga wasu nasarorin da aka samu a baya a ofisoshin ‘yansanda na kananan hukumomi.”

Sanarwar ta ce a wani bangare, “A Nguru, an kama wasu mutum biyu, Jarma Hussaini Adam, mai shekaru 25, da Mohammed Abdusalam, mai shekaru 16, bisa zargin kai wa wani dan sanda hari wanda ke aiki a Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya. A ranar 26 ga Satumba, 2025, an same shi CPL Amani Ali ba tare da hayyacinsa ba tare da jininsa yana zuba, kuma an sace bindigarsa.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

An gudanar da wani samame na musamman wanda ya kai ga gano bindigar da kuma cafke wadanda ake zargin. Jami’in da ya jikkata yana karbar magani a halin yanzu.”

“A Damaturu, jami’an sashen A’ na Hedkwatar ‘Yansanda sun cafke Ibrahim Alhaji Ahmadu, mai shekaru 24, bisa zargin shiga gona da dabbobi da kuma yi wa wani manomi barazana da bindiga. An kwato bindiga mai kananan harsasai daga hannunsa. Rundunar ta jaddada cewa mallaka da amfani da makamai wajen tsoratar da fararen hula babban laifi ne.”

Haka kuma, rundunar ta bayyana cewa, “A Potiskum, an kama Dahiru Ali, mai shekaru 19, bisa zargin lalata da wata yarinya ‘yar shekara uku. Bincike ya gano cewa wanda ake zargin ya taba aikata irin wannan laifi a kan wata yarinya ‘yar shekara uku a unguwar guda. Ya amsa laifinsa, kuma bincike na ci gaba.”

Kwamishinan ‘Yansanda, Emmanuel Ado, ya yi karfafa suka kan wadannan laifuka, inda ya jaddada matsayin rundunar na rashin sassauci kan aikata miyagun laifuka. Ya gargadi masu aikata laifi da su daina, in ba haka ba za su fuskanci mataki mai tsauri, tare da rokon iyaye da masu kula da yara su “rika kula da ‘ya’yansu sosai domin kare su daga batattu.”

CP din ya kuma sake jaddada kiran da yake yi ga iyaye da masu kula da yara da su kara tsaurara kulawa kan ‘ya’yansu don kare su daga masu yi wa yara barna, tare da rokon jama’ar jihar da su ci gaba da ba wa ‘yansanda goyon baya ta hanyar ba da bayanai cikin lokaci don tabbatar da tsaro da aminci ga kowa a jihar.

Yobe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami'an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.