• English
  • Business News
Friday, May 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Karkatar Da Biliyan 2.8: Gwamnatin Kano Ta Maka Sule Garo Da ‘Yan Uwansa Biyu A Kotu

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Gwamnan kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Kano ta gurfanar da tsohon kwamishinan kananan hukumomi, Murtala Sule-Garo da ‘yan uwansa biyu, Mustapha Sule-Garo da Mohammed Sule-Garo kan zargin karkatar da kudaden kananan hukumomi har Naira biliyan 2.8.

A karar da babban lauyan gwamnatin jihar kuma kwamishinan shari’a ya shigar, ta hannun lauyansa, Auwal AbdulQadir-Sani, ya zargi wanda ake tuhuma da amfani da kudaden wajen siyan kadarori a kasar Saudiyya.

  • Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Sabbin Tuhume-tuhume Kan Ganduje Da Kwamishinansa
  • Matsalar Karancin Abinci Za Ta Ƙare Nan Ba Da Jimawa Ba – Gwamnatin Tarayya

A bisa tuhume-tuhume da aka shigar a babbar kotun jihar Kano, gwamnatin jihar ta yi zargin cewa, an karkatar da kudaden ne daga asusun gudanar da kananan hukumomi da kuma kashi daya bisa dari na kudaden bayar da horo.

Auwal ya ce, an shigar da karar ne a karkashin sashe na 211 na kundin tsarin mulkin 1999 da aka yi wa kwaskwarima da kuma sashe na 121 [1], 123 [1] [a], 126 [b], da 377 na dokar shari’a ta jihar Kano [2019].

Mutane bakwai ne ake tuhuma a karar da suka hada da tsohon kwamishinan da ‘yan uwansa biyu da wani ma’aikacin ma’aikatar kananan hukumomi da kamfanoni biyu.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Ta’adda 13,500 Aka Kashe Cikin Shekaru 2 – NSA Ribadu

Ramuwar Gayya: Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Yawa A Borno


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dambarwar siyasar NijeriyaGandujekano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Yi Watsi da Buƙatar Emefiele Na Tafiya Birtaniya Duba Lafiyarsa

Next Post

Kasuwar Hayakin Carbon Ta Kasar Sin Tana Da Karko

Related

Ƴan Ta’adda 13,500 Aka Kashe Cikin Shekaru 2 – NSA Ribadu
Tsaro

Ƴan Ta’adda 13,500 Aka Kashe Cikin Shekaru 2 – NSA Ribadu

2 hours ago
Ramuwar Gayya: Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Yawa A Borno
Labarai

Ramuwar Gayya: Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Yawa A Borno

3 hours ago
Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
Manyan Labarai

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

3 hours ago
Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya
Manyan Labarai

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

4 hours ago
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Labarai

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

13 hours ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

15 hours ago
Next Post
Kasuwar Hayakin Carbon Ta Kasar Sin Tana Da Karko

Kasuwar Hayakin Carbon Ta Kasar Sin Tana Da Karko

LABARAI MASU NASABA

Goron Sallah

GORON JUMA’A

May 23, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

May 23, 2025
Ƴan Ta’adda 13,500 Aka Kashe Cikin Shekaru 2 – NSA Ribadu

Ƴan Ta’adda 13,500 Aka Kashe Cikin Shekaru 2 – NSA Ribadu

May 23, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

May 23, 2025
Ramuwar Gayya: Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Yawa A Borno

Ramuwar Gayya: Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Yawa A Borno

May 23, 2025
Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

May 23, 2025
Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

May 23, 2025
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

May 22, 2025
Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

May 22, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.