• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Ɓata-gari Na Iya Amfani Da Zanga-zanga Domin Tada Zaune Tsaye – Minista

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Wasu Ɓata-gari Na Iya Amfani Da Zanga-zanga Domin Tada Zaune Tsaye – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya tana sane da cewa, wasu mutane na son yin amfani da zanga-zangar da ake shirin yi wajen tayar da tarzoma kan ‘yan Nijeriyar da ba su ji ba ba su gani ba.

 

Ya ce, duk da yake gwamnatin Shugaba Tinubu ta amince da ‘yancin kowane ɗan Nijeriya na gudanar da zanga-zanga, ta duƙufa wajen ganin cewa waɗannan ayyuka ba su kawo cikas ga zaman lafiyar jama’a ko take haƙƙin wasu ba.

  • Gwamnati Ba Za Ta Yi Amfani Da Karfi Ba Akan Masu Zanga-zanga – Minista
  • Zanga-zangar Matsin Rayuwa: Gwamnoni Sun Gana Da Ribadu Kan Sha’anin Tsaro

Idris ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin shugabannin Ƙungiyar Charismatic Bishops a wata ziyarar ban-girma da suka kai ofishin sa da ke Abuja a ranar Laraba.

 

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

A wata sanarwa da Mataimaki na Musamman ga Ministan kan Harkokin Watsa Labarai, Malam Rabi’u Ibrahim ya fitar, ministan ya ce: “Gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta amince da ‘yancin kowa da kowa a cikin tsarin doka ya yi abin da yake ganin ya dace a gare shi. Don haka Shugaban Ƙasa ba ya adawa da kowace irin zanga-zanga amma Shugaban Ƙasa na adawa da tashin hankali da duk wani abu da zai taɓa lafiyar ‘yan Nijeriya.

 

“Ya yi imani kuma ya kasance yana cewa a cikin tsarin dimokiraɗiyya, kuna da ‘yancin yin duk abin da kuke so idan har wannan haƙƙin bai take haƙƙin wani ba.

 

“Dalilin da ya sa kowa yake taka-tsantsan kuma ya gaji da wannan zanga-zangar ta ƙasa saboda mun ga abin da ya faru a wasu ƙasashen ne. Mun san cewa da wuya a gudanar da wannan zanga-zangar kuma a samu zaman lafiya. Ba za mu yarda da hakan ba saboda wasu mutane suna jira su ɗauki doka a hannun su ”

 

Idris ya bayyana cewa Shugaba Tinubu yana da cikakkiyar masaniya game da damuwa da ƙorafe-ƙorafe da ‘yan Nijeriya ke yi a faɗin ƙasar nan, kuma ya himmatu wajen aiwatar da ingantattun manufofi da nufin magance matsalolin da ‘yan ƙasa ke fuskanta da kuma kawo sassauci ga ɗaukacin ‘yan Nijeriya.

 

Ministan ya ce a wani mataki da ba a taɓa ganin irin sa ba, Shugaba Tinubu yana tsara tsarin biyan alawus-alawus ga dukkan matasan da suka kammala karatu a jami’a da kwalejin kimiyya da fasaha kafin su samu aikin yi.

 

Ya ce: “Kuma bayan haka, akwai wani sabon tsari da Shugaban Ƙasa ya yi, wanda za a fara ganin sa nan ba da daɗewa ba, wato duk matasa maza da mata da suka kammala jami’a da kwalejin kimiyya da fasaha kuma suna da takardar shaida kuma sun yi bautar ƙasa (NYSC) ba su samu aikin yi ba, za su samu wani abu daga gwamnati da za su ci gaba da rayuwa har sai lokacin da suka samu aikin yi.”

 

Ya bayyana cewa saboda jajircewar da Shugaban Ƙasar ya yi wajen kyautata rayuwar ma’aikatan Nijeriya, ko da kwamitin da ke kula da mafi ƙarancin albashi na ƙasa ya kammala aikin sa tare da miƙa rahoton sa, shugaban ya ci gaba da tattaunawa da ƙungiyoyin ƙwadago har sai da aka cimma matsaya na mafi ƙarancin albashi na ƙasa naira 70,000.

 

Idris ya ce ɓullo da shirin iskar gas na CNG da Shugaban Ƙasa ya yi yana kawo sauyi a tattalin arzikin ƙasar saboda yadda ya rage kuɗin sufuri da kusan kashi 60.

 

Ya kuma bayyana irin cigaban da aka samu a harkar tsaro, inda ya ce tun zuwan gwamnatin Tinubu, an samu gagarumin cigaba a mafi yawan wuraren da ake tashe-tashen hankula, musamman a babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna.

 

A nasa jawabin, Shugaban ƙungiyar Kiristoci ta Charismatic Bishops, Archbishop Leonard Kawas, ya nesanta ƙungiyar da shirin gudanar da zanga-zangar, yana mai cewa wasu ƙungiyoyi sun tuntuɓe su domin shiga zanga-zangar.

 

Ya ce: “Mai girma Minista, a kwanan baya mun samu wasu kiraye-kiraye daga wasu ƙungiyoyin addini da sauran ƙungiyoyi suna neman mu shiga cikin shirin gudanar da zanga-zanga a faɗin ƙasar nan, wanda za a fara daga ranar 1 ga Agusta, 2024.

 

“Mun zo nan ne domin mu sanar da kai cewa ba ma tunanin haka. Mun gwammace mu yi kira da a yi sulhu.

 

“Mun yanke shawarar mu yi roƙo da a zauna lafiya tare da neman ’yan’uwan mu da aka yi wa ba daidai ba ta kowace hanya, su ba mu lokaci mu ci gaba da tattaunawa da wannan gwamnati a kan abubuwan da suka shafe su.”

 

Ya ce bayan Taron Coci na 2024, sun yanke shawarar yin haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya wajen yin addu’o’i da bayar da shawarwari domin samun nasarar gwamnatin Tinubu.

 

Archbishop Kawas ya tabbatar da cewa gwamnatin ta samu gagarumin cigaba a fannin zuba jari a cikin al’umma, ɓullo da Shirin Lamuni na Ɗalibai, tsaro, samar da ababen more rayuwa a Babban Birnin Tarayya, da kuma ƙaddamar da mafi ƙarancin albashi na naira 70,000, da dai sauran su.

 

Har ila yau, Ƙungiyar Charismatic Bishops ta yi amfani da ziyarar ta ba da lambar yabo ta hidima ga Minista Idris.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Gudanar Da Tattaunawa Kan “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya” A kasashen Najeriya Da Afirka Ta Kudu Da Zambiya

Next Post

Zanga-zanga: Tinubu Ya Yi Taron Gaggawa Da Manyan Sarakunan Gargajiya A Abuja

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

50 minutes ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

3 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

5 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

6 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

7 hours ago
Next Post
Zanga-zanga: Tinubu Ya Yi Taron Gaggawa Da Manyan Sarakunan Gargajiya A Abuja

Zanga-zanga: Tinubu Ya Yi Taron Gaggawa Da Manyan Sarakunan Gargajiya A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.