• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Don Hana Zanga-Zanga, Shugaba Tinubu Ya Amince Da Kafa Ofishin Matasa A Abuja

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Zanga-Zanga

Shugaba Bola Tinubu ya amince da kafa ma’aikatar harkokin Matasa a Abuja (FCT), a cewar Ministan babban birnin tarayya Nyesom Wike. An bayyana hakan ne yayin wata ganawa da mazauna ƙaramar hukumar Bwari, a wani yunkuri na Minista Wike na ci gaba da samar da zaman lafiya a yayin da ake shirin gudanar da zanga-zangar ƙasa baki ɗaya daga 1 zuwa 10 ga watan Agusta.

Wannan ganawar ta biyo bayan wasu tattaunawar a baya da aka yi a Gwagwalada, da Kuje, da Kwali, da ƙaramar hukumar birnin Abuja (AMAC), da Abaji don hana matasa shiga zanga-zangar.

  • Zanga-Zanga: Sojoji Sun Karɓe Iko Da Tsaron Hanyar Shiga Abuja
  • An Tona Asirin Masu Yi Wa Matatar Dangote Zangon Ƙasa

Wike ya amince da wannan buƙata ne a lokacin da matasan AMAC suka gabatar masa da ita, wanda ya yi alƙawarin tattaunawa da Shugaba Tinubu. Ministan ya tabbatar da amincewar a lokacin ganawar a Bwari, yana mai jaddada ƙudirin gwamnati na tabbatar da haɗin kan matasa da bunƙasa su. Ya yaba wa matasan bisa kin shiga zanga-zangar da ake shirin yi, yana ganin wannan mataki na nuna hazaƙa da goyon bayan gwamnati ne. Wike ya kuma tabbatar wa mazauna yankin cewa za a ci gaba da inganta ababen more rayuwa, tare da kammala ayyukan hanyoyi a garuruwan wajen FCT nan da Disamba 2024.

A nasa jawabin, Mista Ezekiel Dalhatu, wanda ya wakilci ƙungiyar masu ruwa da tsaki ta Matasa da haɗin gwuiwar dukkan ƙungiyoyin matasa a FCT, ya tabbatar da cewa matasa sun yanke shawarar shiga tattaunawa maimakon zanga-zanga.

Ya jaddada muhimmancin tattaunawa mai ma’ana da gwamnati don magance matsalolinsu. Shugaban ƙaramar hukumar Bwari, Mista John Gabaya, ya yi kira ga matasa da su rungumi tattaunawa, yana mai tabbatar wa Wike da goyon bayan mazauna FCT.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

An kammala zaman ne da gabatar da hoton girmamawa na Wike daga matasa da sauran masu ruwa da tsaki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Next Post
Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar

Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.