• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin 3MTT Zai Samar Wa Matasa Miliyan Uku Aikin Yi, inji Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
1 year ago
Amurka

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa, gwamnatin Tinubu ta shirya tsaf don samar da ayyukan yi miliyan uku ga matasan Nijeriya ta hanyar Shirin 3MTT.

 

Ministan ya bayyana hakan ne a Abuja ranar Litinin a Taron Matasa ‘Yansandan Nijeriya mai taken “Inganta Ƙimar Matasan Nijeriya don Tsaron Ƙasa.”

  • Nijeriya Ta Fara Sayar Da Makaman Da Ta Ke Kerawa – Minista
  • Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi

Ministan, wanda ya samu wakilcin Darakta Janar na hukumar gidan rediyon Muryar Nijeriya (VoN), Malam Jibrin Baba Ndace, ya ce shirin na 3MTT, wanda Ma’aikatar Sadarwa ke jagoranta, wani shiri ne na ilimi da ƙwarewar da za su inganta iyawa da ƙimar matasa a harkar tsaron ƙasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Ya ce: “Shirin 3MTT tabbaci ne na burin Shugaba Tinubu na samar da cigaban matasa a cikin dabarun cigaban ƙasa baki ɗaya. Domin samar da kyakkyawan tsari don cimma wannan, gwamnatin tana kuma ba da fifiko ga tattalin arzikin matasan Nijeriya, wajen gina ƙasa mai tsaro da wadata.”

 

Idris ya ce kafa Asusun Ba Da Lamuni na Ilimi na Nijeriya (NELFUND), wanda a halin yanzu yake bayar da lamuni da tallafin kuɗi ga ɗaliban Nijeriya, yana ɗaya daga cikin manyan tsare-tsare a ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata na Shugaba Tinubu, da nufin yin tasiri sosai kan neman ilimi na matasa.

 

A yayin da yake magana kan tsadar sufuri a ƙasar nan, ministan ya ce Shugaban Ƙasa ya ɓullo da shirin CNG don amfani da isasshiyar iskar gas da ƙasar ke da ita wajen rage farashin sufuri da kusan kashi 70.

 

Ministan ya kuma jaddada buƙatar da ke akwai ta matasa su yi koyi da kyawawan ɗabi’un da suka dace domin su taka rawar su a harkar tsaron ƙasa.

 

Sai dai ministan ya gargaɗi matasa kan illolin da yaɗa labaran ƙarya ke da shi ga tsaron ƙasa, yana mai cewa wannan muguwar ɗabi’a amfani da ‘yancin faɗin albarkacin baki, wanda gwamnati mai ci yanzu ta amince da shi, ta hanyar da ba ta dace ba ne.

 

Ya ce: “Inda aka ba da yawa, ana sa ran da yawa. Dole ne mu yarda cewa yaɗa labaran ƙarya ya haɗu da babbar barazana ga tsaron ƙasa, wadda ta haɗa da tada hankali, rashin zaman lafiya, laifuffuka na ƙasa da ƙasa, ta’addanci, fashi da makami, tsattsauran ra’ayi, da munanan ayyukan da ake yaɗawa ta hanyar intanet.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Asuu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro
Labarai

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
majalisar kasa
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
Next Post
Cinikayyar Sin Da Afirka Ta Bunkasa Bisa Daidaito Tsakanin Janairu Da Yuli

Cinikayyar Sin Da Afirka Ta Bunkasa Bisa Daidaito Tsakanin Janairu Da Yuli

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.