• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Da Ba Za Su Iya Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Naira 70,000 A Nijeriya

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnonin Da Ba Za Su Iya Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Naira 70,000 A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da Shugaba Bola Tinubu ya gabatar da sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000, wasu gwamnonin jihohin Nijeriya, sun bayyana cewa ba za su iya biyan wannan sabon albashin ba saboda matsalolin kudi. 

Ga jerin gwamnonin:

  • Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma’ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin
  • Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu

Jihar Gombe: Gwamna Inuwa Yahaya

Gwamna Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya ce gwamnatinsa ba za ta iya biyan sabon albashin Naira 70,000 ba saboda kudaden da jihar ke samu daga gwamnatin tarayya ba za su isa ba.

Yahaya, wanda kuma shi ne shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, ya ce biyan tsohon mafi karancin albashi na Naira 30,000 yana yi musu wahala.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Ya bayyana cewa da yawa daga cikin jihohi ba za su iya biyan karin albashin ba, duk da karin kudaden da suka samu daga gwamnatin tarayya a kwanan nan.

Jihar Nasarawa: Gwamna Abdullahi Sule

Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa, ya yanke shawarar jinkirta aiwatar da sabon tsarin mafi albashi na Naira 70,000 har zuwa shekarar 2026.

A baya, ya yi alkawarin fara biyan sabon albashin a wannan watan, tare da biyan bashin watannin da suka wuce.

Duk da haka, ya bayyana cewa jihar na bukatar kimanin Naira miliyan 200 domin biyan ma’aikata, wanda ya ce hakan ba zai yiwuwa jihar ta fara biyan sabon albashin a yanzu ba

Jihar Kogi: Gwamna Ahmed Usman Ododo

Gwamna Ahmed Usman Ododo na Jihar Kogi bai yanke shawara kan ko yaushe gwamnatinsa za ta fara biyan sabon mafi karancin Naira na 70,000 ba.

Kwamishinan kudi na jihar, Ashiwaju Ashiru Idris, ya ce ba a sanya ranar fara biyan sabon albashin ba.

Damuwar Masana’antu Masu Zaman Kansu

Kungiyar Masana’antu Masu Zaman Kansu (OPS), ita ma ta bayyana damuwa kan sabon albashin na Naira 70,000.

Sun ce zai yi wahala kamfanoni su iya biyan wannan sabon albashi ba tare da samun taimako na musamman ba.

Adewale-Smatt Oyerinde, mai magana da yawun Kungiyar Masu Daukar Ma’aikata ta Nijeriya (NECA), ya nuna damuwa kan yadda sabon tsari albashin zai jefa kamfanoni cikin matsalar kudi.

Martanin Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC)

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) a Jihar Legas, ta fayyace cewa mafi karancin albashin Naira 35,000 da ake biya a halin yanzu daban ne da sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000 da mayar doka kwana nan.

Funmi Sessi, shugaban NLC na Jihar Legas, ya yi kira da a samar da tsarin albashin da ya dace da nau’ikan ayyuka da matakan albashi daban-daban.

Wannan yanayin ya bayyana matsalolin kudi da jihohi da masana’antu daban-daban ke fuskanta wajen kokarin gyara tsarin albashinsu zuwa sabon mafi karancin albashi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GwamnoniLabaraiMa'aikataMafi Karancin Albashi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma’ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin

Next Post

Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

6 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

11 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

12 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

13 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

14 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

15 hours ago
Next Post
Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.