• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Da Ba Za Su Iya Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Naira 70,000 A Nijeriya

by Sadiq
11 months ago
in Labarai
0
Gwamnonin Da Ba Za Su Iya Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Naira 70,000 A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da Shugaba Bola Tinubu ya gabatar da sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000, wasu gwamnonin jihohin Nijeriya, sun bayyana cewa ba za su iya biyan wannan sabon albashin ba saboda matsalolin kudi. 

Ga jerin gwamnonin:

  • Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma’ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin
  • Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu

Jihar Gombe: Gwamna Inuwa Yahaya

Gwamna Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya ce gwamnatinsa ba za ta iya biyan sabon albashin Naira 70,000 ba saboda kudaden da jihar ke samu daga gwamnatin tarayya ba za su isa ba.

Yahaya, wanda kuma shi ne shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, ya ce biyan tsohon mafi karancin albashi na Naira 30,000 yana yi musu wahala.

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Ya bayyana cewa da yawa daga cikin jihohi ba za su iya biyan karin albashin ba, duk da karin kudaden da suka samu daga gwamnatin tarayya a kwanan nan.

Jihar Nasarawa: Gwamna Abdullahi Sule

Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa, ya yanke shawarar jinkirta aiwatar da sabon tsarin mafi albashi na Naira 70,000 har zuwa shekarar 2026.

A baya, ya yi alkawarin fara biyan sabon albashin a wannan watan, tare da biyan bashin watannin da suka wuce.

Duk da haka, ya bayyana cewa jihar na bukatar kimanin Naira miliyan 200 domin biyan ma’aikata, wanda ya ce hakan ba zai yiwuwa jihar ta fara biyan sabon albashin a yanzu ba

Jihar Kogi: Gwamna Ahmed Usman Ododo

Gwamna Ahmed Usman Ododo na Jihar Kogi bai yanke shawara kan ko yaushe gwamnatinsa za ta fara biyan sabon mafi karancin Naira na 70,000 ba.

Kwamishinan kudi na jihar, Ashiwaju Ashiru Idris, ya ce ba a sanya ranar fara biyan sabon albashin ba.

Damuwar Masana’antu Masu Zaman Kansu

Kungiyar Masana’antu Masu Zaman Kansu (OPS), ita ma ta bayyana damuwa kan sabon albashin na Naira 70,000.

Sun ce zai yi wahala kamfanoni su iya biyan wannan sabon albashi ba tare da samun taimako na musamman ba.

Adewale-Smatt Oyerinde, mai magana da yawun Kungiyar Masu Daukar Ma’aikata ta Nijeriya (NECA), ya nuna damuwa kan yadda sabon tsari albashin zai jefa kamfanoni cikin matsalar kudi.

Martanin Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC)

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) a Jihar Legas, ta fayyace cewa mafi karancin albashin Naira 35,000 da ake biya a halin yanzu daban ne da sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000 da mayar doka kwana nan.

Funmi Sessi, shugaban NLC na Jihar Legas, ya yi kira da a samar da tsarin albashin da ya dace da nau’ikan ayyuka da matakan albashi daban-daban.

Wannan yanayin ya bayyana matsalolin kudi da jihohi da masana’antu daban-daban ke fuskanta wajen kokarin gyara tsarin albashinsu zuwa sabon mafi karancin albashi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GwamnoniLabaraiMa'aikataMafi Karancin Albashi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma’ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin

Next Post

Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

55 minutes ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

3 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

3 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

4 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

7 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

9 hours ago
Next Post
Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.