• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Mayar Da Talaka Saniyar Ware (Nazari)

by Murtala Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Kokarin Mayar Da Talaka Saniyar Ware (Nazari)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A lokacin da duniya ke ci gaba ta fuskar ilimin kimiyya da fasaha, tattalin arziki, kiwon lafiya da zamantakewar Dan’adam ta fuskar tsaron rayuwa da dukiyoyin al’umma, ita kuma Nijeriya abin ba haka yake ba.

Ilimi ya zama koma-baya, wanda ilimi shi ya kamata ya zama a sahun farko a duk kasar da take son ta ciyar da al’ummarta gaba, kiwon lafiya kuma ya zamo hanyar da ‘yan siyasa ke bi don kwasar baitulmalin gwamnati a canza ta zuwa lalitar kashin kansu don son rai da rashin sanin hakin da ya rataya a wuyan su.

Idan ba a manta ba, Uwargidan Shugaban Kasar Nijeriya ta fito kafafen yada labarai ta shelanta cewa, asibitin fadar shugaban kasa babu ko sirinji ballantana a yi maganar magunguna na tsaron lafiya, kuma duk shekara ana fitar da kasafin makudan kudaden wannan asibiti.

Ta fuskar tsaro kuma ya zama wata hanya ta sace lalitar gwamnati da sunan tsaro, wanda har yanzu tsaron kullum tabarbarewa yake.

A yau muna cikin wata na hudu da sace al’ummar Nijeriya a cikin jirgin kasan da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna, ta kai matsayin da wani matashi a cikin fasinjojin da aka sace ke korafin cewa ‘yan’uwansu na son su karbo su, amma gwamnati ta hana, ita kuma gwamnatin babu wani hobbasa da take yi domin ceto su, kuma an kai wani matakin da ‘yan ta’addan ke azabtar da fasinjojin da suke tsare da su.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

A Nijeriya ne kuma aka samu babban ma’ajin gwamnati wato ‘Accountant General’ da harshen Turanci da ake zargi da satar kudin gwamnati da ya kai kimanin naira biliyan 109 tare da gudunmuwar wasu daga cikin abokan aikinsa ko kuma a ce yaransa, wanda shi ma’ajin nan shi ne ummul’aba’isan shigar jami’o’in kasar nan yajin aiki, to Allah ya kyauta.

Haka kuma an samu jami’in tsaro kuma babban dan sanda mai matsayin mataimakin babban sufeton ‘yan sanda a hukumar rundunar ‘yan sandan Nijeriya da ake zargi da hannu dumu-dumu a safarar muyagun kwayoyi da hada kai da muggan masu zambo cikin aminci da dukiyoyin al’umma, Allah ya kyauta.

A siyasance kuma, duk magoya bayanka idan har kai ba dan takarar da gwamnati ke goyon baya ba ne, babu kai a jerin sunayen da za a mika wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), misali kamar yadda ya kasance a Jihar Kano, duk dan takarar da ba yaron gwamna ba ne a bai samu tikitin tsayawa takara ba, wanda hakan ya zama dalilin da ya sa mafiya yawa daga cikin ‘yan jam’iyyar gwamnati sauya sheka zuwa wasu jam’iyyun siyasa.

Ta fuskar ilimin jami’o’i kasar nan kuma, yau jami’o’in da suke mallakar gwamnatin Nijeriya su ne koma-baya har ta kai matsayin da sun tafi yajin aikin da babu wani da ya san yaushe za su dawo, wanda kungiyar kwadago ta gudanar da zanga-zanga, inda gwamnatin ta yi ta kokarin hana wannan zanga-zanga ya gudana amma abin ya ci tura.

Abin da mahukuntan gwamnati suke mantawa shi ne, kullum kara hura wutar bakin jini suke tsakanin jami’an gwamnati da talakawan kasar nan, an kai matakin da ko wane talaka ya san cewa gwamnatin da ya bai wa gudunmuwa ta kudi da ta jajircewa wajen ganin ta cimma nasara, yau nasarar ta samu kuma shi talaka ya zama saniyar ware a kan komai, shi ba ga noma gonakin da suka gada wajen iyaye da kakanni ba, shi ba ga kasuwanci ba, an hana shi zaman lafiya a ko’ina, babu tsaro, abinci ya yi tsada, rayuwa ta yi wahala, wanda su kuma mahukuntan kasar hankalinsu a kwance yake tamkar babu wani abu da ke faruwa, rayukan talakawa ya zama abin ko-in-kula.

Babu wanda yake damuwa don an kashe mutane a arewacin kasar nan, amma kuma idan aka kashe mutum daya a kudancin kasar nan, a lokacin ne za ka ga hankalin gwamnati ya tashi, kamar kudancin kasar nan ne kadai mutane.
A da ana matakin da sai a kan hanya ake tare mutane a yi musu fashi da makami, aka zo matakin da ake sace mutane a kudancin Nijeriya, wanda a lokacin Marigayi Sam Nda-Isaiah yake kira da babbar murya a shafinsa da yake fitowa duk ranar Litinin a Jaridar LEADERSHIP, ka da a sake a bai wa mutanen arewa damar da za su iya abin da ake kira da harshen turanci ‘Kidnapping,’ domin idan hakan ta faru abin ba zai yi kyau ba.

 

Amma an bar ginin tun ranar zane, yanzu mutanen arewa sun iya, kuma ya zama ruwan dare gama duniya ko’ina a arewan, babu inda ba a sace mutane ba.

Ya kamata gwamnatin Nijeriya ta waiwayo talakawa ta san cewa talakawan Nijeriya sun bayar da gudunmuwar wajen kafa wannan gwamnati.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Likitoci Sun Bude Kungiyar Kula Da Marasa Lafiya Kyauta A Abuja

Next Post

Bukatar Sa Ido A Kan Abokan Huldar Yaranmu

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

8 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

9 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

10 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

11 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

13 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

15 hours ago
Next Post
Bukatar Sa Ido A Kan Abokan Huldar Yaranmu

Bukatar Sa Ido A Kan Abokan Huldar Yaranmu

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.