• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Kasar Sin: Yabon Gwani Ya Zama Dole

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Kasar Sin: Yabon Gwani Ya Zama Dole
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban yankin Zanzibar na kasar Tanzaniya, Hussein Ali Mwinyi ya ba da lambobin yabo da takardun shaidar karramawa ga daukacin mambobin tawaga ta 33 ta jami’an lafiya na Sin, da suka bayar da gudunmawar jinya da kiwon lafiya a Zanzibar.

 

Kiwon lafiya daya ne daga cikin bangarorin da Sin take hadin gwiwa da kasashen Afrika, inda ta kan tura jami’ai akai-akai domin bada tallafin jinya da horo kyauta. Hadin gwiwar kasar Sin ba abu ne dake mayar da hankali kan moriyarta kadai ba, sabanin yadda wasu suke yada jita jita ko ma suke yi, kasar Sin ta kan taimaka ta kowane bangare da take ganin kasashe masu tasowa, musamman na Afrika na da bukata domin ganin sun samu ci gaba.

  • Wang Yi Da Jake Sullivan Sun Gudanar Da Sabon Zagaye Na Muhimmin Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka
  • Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

Tun daga shekarar 1963, kasar Sin ta fara tura jami’an kiwon lafiya kasashen duniya. Cikin shekaru 60 da suka gabata, ta tura jami’an da yawansu ya kai 30,000 zuwa kasashe da yankunan duniya 76, tare da jinyar mutane miliyan 290. Kuma yayin da wadannan jami’an lafiya ke zuwa kasashen, su kan tafi da magunguna da kayayyakin jinya da gwaje-gwaje da sauransu, domin tabbatar sun bada ingantaccen kiwon lafiya.

 

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

A kwanakin baya, na hadu da wata kwararriyar likitar ido ta kasar Sin mai suna Dr. Li Yun. Tun daga shekarar 2016, Li Yun ta je nahiyar Afrika sau 4, inda ta gudanar da tiyatar ido fiye da 500. Kuma duk da cewa ta dawo kasar Sin, har yanzu ba ta yanke hulda da kasashen da ta je, har yanzu ta kan tattauna da su ko gudanar da taron karawa juna sani kan abubuwan da suka shige musu duhu.

 

Yanzu haka akwai tawagogin lafiya na Sin dake aiki a wurare 115 dake kasashe 56 na fadin duniya, kuma galinbinsu wurare ne masu nisa da koma baya. Duba da irin ci gaban kasar Sin da kyautatuwar yanayin rayuwa, wadannan jami’ai sun cancanci yabo matuka, domin sun sadaukar da kansu da jin dadinsu wajen ganin sun taimakawa burin kasarsu na ganin ta taimakawa masu bukata. A kullum na kan ce, daya daga cikin tubalin ci gaban kasar Sin shi ne, yadda al’ummarta ke da kishi da kaunar kasarsu da kuma kyakkyawar fahimta da hadin gwiwa dake akwai tsakanin gwamnati da al’umma. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NIREC Ta Buƙaci Tinubu Ya Kawo Ƙarshen Rashin Tsaro A Nijeriya

Next Post

Tinubu Zai Kai Ziyara Kasar Sin Domin Haɓaka Tattalin Arziki  Da Kayayyakin More Rayuwa 

Related

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

10 hours ago
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

11 hours ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

12 hours ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

13 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

14 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

16 hours ago
Next Post
Tinubu Zai Kai Ziyara Kasar Sin Domin Haɓaka Tattalin Arziki  Da Kayayyakin More Rayuwa 

Tinubu Zai Kai Ziyara Kasar Sin Domin Haɓaka Tattalin Arziki  Da Kayayyakin More Rayuwa 

LABARAI MASU NASABA

Sin

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.