ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

by Ra'ayinmu
10 months ago
Albashi

A kwanan baya ne, Hukumar Raba daidai ta ƙasa, ta shelanta cewa, za ta yiwa ƴ an siyasa, masu riƙe da
madafun iko, ƙarin albashin, inda wannan batun, ya haifar da ce-ce kuce da kuma suka daga ɓangarori da
dama, na ƙasar.
Sukar dai, ta biyo bayan ganin cewa, ƙarin bai da ce, duba da irin matsin tattalin arziki, da ya yiwa ƙasar
ɗaurin Demom Minti da ci ga da fuskatar hauhawan farashin kayan masarufi, musamman kayan abinci da
giɓin da aka samu, a cikin kasafin kuɗin ƙasar da kuma irin halin ƙunci rayuwa, musamman da talakawan ƙasar, suka tsinci kansu a ciki.

  • Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Nijeriya Sun Koka Kan Rashin Biyan Basussukan Albashi
  • Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da Karɓar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa
    Sai dai, Hukumar ta kafa hujja da cewa, ƙarin ya zama wajibi, musamman domin tun a shekarar 2008, shugaba ƙasa har yanzu, na karɓar Naira miliyan 1.5 a duk wata, a matsayin albashi inda ministoci, ke karɓar ƙasa da Naira miliyan ɗaya, a duk wata, a matsayin albashi.

Kazalika, Hukumar ta tage kai da fata cewa, wannan jeren albashin, ya yi ƙaranci matuƙa, duba da
hauhawan farashin kaya a ƙasar da kuma tsadar rayuwa.
A cewar Hukumar akwai matuƙar banbanci kan albashin da ake biyan masu riƙe da madafun ikon na
siyasa, da kuma na sauran shugabannin Hukumin Gwamnati, musamman dai, albashi kamar na Darakta- Janar da na cibiyoyin kuɗi, kamar irinsu Babban Bankin Nijeriya, waɗanda albashinsu, ya ɗara na
shugaban ƙasa da kuma na ministoci.
Amma wannan ya nuna cewa, akasarin masu riƙe da madafun ikon na siyasa, a ƙasar, sun fi samun kuɗaɗen shiga ne ta hanyar alawus-alawus da suke samu.
Misali, a duk wata, Sanata ɗaya na samun alawus da ya kai sama da Naira miliyan 21, wasu ƴ an majlisar, a shekara ɗaya, suke samun alawus da ya kai na Naira 500 da sunan na ayyukan da suke gudanarwa, a
mazaɓunsu, wanda ba a sanya wannan, a lissafi.

Bugu da ƙari, akwai kuma sauran wasu kuɗaɗen shiga da ƴ an siyasar, masu riƙe da madafun iko suke samu, waɗanda suka haɗa da na gidajen kwanansu da na tafiye-tafiyensu da na tsaronsu da kuma na sauran wasu damarmaki, wanda wannan, ya ɗara kuɗaɗen shiga, da ma’aikatan gwamnati suke samu da kuma na sauran fannoni da ban da ban.Wannan batun na cewa, ana biyan ƴ an siyasar masu riƙe da madafun ikon, kuɗaɗen da ba su taka Kara sun karya ba, za a iya cewa, wani yunƙuri ne, na karkatar da kan alumma da kuma yunƙurin chusawa, ƴan Nijeriya, rashin yarda a Zukakansu. A zahirance, tuni a Nijeriya aka mayar da muƙaman siyasa zuwa wata haynya ta hada-hadar cinikayya,
mai makon a mayar da hankali, wajen inganta rayuwar ƴ an ƙasa.

ADVERTISEMENT

Hakan ne ya ke sanya, ko ta halin ƙaƙa, a lokacin da ta zaɓe ya ƙarato, wasu masu son sake ci gaba da riƙe muƙamansu, suke tayar da hargitsi ko kuma kashe ɗimbin biliyoyin Naira, domin kawai, su sake
lashe zaɓe.

A daidai wannan lokacin ne, da Hukumar ke son ganin an yiwa ƴ an siyasar masu riƙe da madafun ikon,
hakan ya zaburar da ƙungiyoyi kamar su na ƙwadago da ƙunƙiyar tuntuɓa ta Arewacin ƙasar wato ACF da ƙungiyar da ke kare muradun jama’ar Arewa ta tsakiya wato MBF, suka fara yin suka da kuma yin tir, kan wannan yunƙurin na ƙarin wanda suka alƙanta shi, a matsayin son rai da nuna handama.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kazalika, masu sukar na ganin cewa, gwamnatin ta yi watsi da irin halin ƙuncin rayuwa da musamman
talakwan ƙasar, ke ci gaba da fuskanta, kamar dai, na ci gaba da hauhawan farashin kayan masarufi da
ƙarin kuɗin Man Fetur da ƙarin kuɗin wutar lantarki da ƙarancin albashin da ake biyan ma’aikata, musamman na gwamnati, wanda a baya, ta yi alƙawarin lalubo masu da mafita.

Wannan batun na ƙarin albashin, tamkar dai wani cin zarafi wanda kuma abu ne, da ke tattare da hatsari.
Kusan tun lokacin da shugaba Bola Tinubu, ya ɗare Karagar shugabancin ƙasar, ya rage yawan kuɗaɗen
da ake kashewa, na gudanar da mulki, inda gwamtainsa, ta rage yawan ɗimbin tawagar da take kwasa, na
yin tafiye-tafiye, musamman zuwa ƙasashen duniya.
Amma batun na ƙarawa ƴ an siyasa masu riƙe da madafun ikon, a wannan yanayin da ƙasar ke a ciki, tamkar mayar da Agogo baya ne.
Misali, gwamnatin har zuwa yau, ta gaza wajen cika ɗaukacin buƙatun ƙungiyoyin manyan makaratun
ƙasar wato ASU da kuma ASUP, inda kuma a gefe ɗaya, ƙungiyoyin ƙwarrun likitoci, suma suke ta kai gwauro da mari, na neman gwamnatin, ta biya masu na su buƙatun
Saboda rashin biya masu buƙatun na su, suke tsunduma cikin yajin aiki na gargaɗi ko kuma gargaɗi.

Hakazalik, a yayin da ƙasar ke jigelon kashe kuɗaɗe, na gudanar da wasu ayyuka a ƙetare, amma a gife
ɗaya, an bar ma’aikata na karɓar mafi ƙarancin alabshin na Naira 70,000 kacal, inda wannan kuɗin, ba zai
iya kawar masu koda da ƙishirwarsu ba, duba da hauhawan kayan masarufi, da ake ci gaba da fuskanta a
ƙasar.

Akasarin ma’aikata a ƙasar, na ci gaba da kasance wa ne a cikin talauci, inda kuma sauran ƴ an siyasa, ke ci gaba da yin wadaƙa.
Maimakon ƙarin albashin kamata yi Hukumar ta fara tunanin fara yiwa albashin ma’aikatan gwamnati
garanbawul da kuma inganta rayuwarsu.A yayin da ƙasar ke ci gaba da fuskantar ƙaranci kuɗi tare da kuma yadda alummar ƙasarke ci gaba da
fitar da rai ga alƙawarin da gwamnatin shugaba Tinubu ta yi, na saita ƙasar, batun na yin ƙarin, a wannan
lokacin, wani abin dubawa ne.
Wannna Jaridar ta nuna takaicinta kan wannan batun, musamman duba da cewa, yunƙurin na Hukumar, na ci gaba da fuskantar suka.

Bugu da ƙari, duba da cewa, Nijeriya kusan ta dogara ne kachokam, kan ciwao bashi daga ƙetare, domin
ci giɓin da take da shi, a cikin kasafin kuɗinta, wanda hakan ya saɓawa ƙa’ida, a saboda haka, batun na
ƙarin albashin ga ƴan siyasa, tamkar zuba kuɗi ne, a inda bai kamata ba.
Ya zama wajibi, gwamnatin ta dakatar da wannan batun na ƙarin albashin ga ƴan siyasa masu riƙe da madafun iko, amma ta mayar da hankali, wajen gudanar da bin diddigin kashe kuɗaɗe wanda zai yi daidai da, tsarin tattalin arzikin ƙasar, a zahirance da kuma gudanar da ƙa’idojin gudanar da aikin gwamnati.

Albashi
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
Next Post
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.