• English
  • Business News
Tuesday, May 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Yi Allah-Wadai Da Kisan Gillar Da Sojoji Suka Yi Wa DPO Wasagu A Kebbi

by Umar Faruk
9 months ago
in Labarai
0
Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Zamfara, ta yi matukar bakin ciki da damuwa game da kisan gillar da aka yi wa Sufiritandan ‘Yansanda Haliru Liman, DPO a ofishin ‘yansanda a garin Wusagu, a Jihar Kebbi.

A ranar 28 ga watan Agusta, 2024, da misalin karfe 10:30 na safe, jami’an soji karkashin wani Hassan, da ke karkashin sashen Operation Hadain Daji, a unguwar Dan Marke a Bukkuyum, Jihar Zamfara, sun harbe SP Liman har lahira.

  • Minista Ya Nemi A Ƙara Ƙulla Danƙon Zumunci A Tsakanin Nijeriya Da Kamfanin BBC
  • Tawagar Jami’an Jihar Guangxi Ta Sin Ta Ziyarci Kasar Niger

Abubuwan da ke tattare da wannan lamarin suna da ban tsoro kuma ba za a yarda da su ba. SP Liman Haliru wanda ke kan hanyarsa ta halartar wani taro na wata-wata a Birnin Kebbi, jami’an soji ne suka tare shi duk da ya bayyana kansa a matsayin dan sanda.

A wani yanayi mai ban tsoro da ya nuna, Hassan ya harbi SP Liman a kai, wanda ya yi sanadiyyar mutuwarsa nan take.

“Muna Allah-wadai da wannan kisan gillar bazata, muna kuma bukatar a gudanar da cikakken bincike a kan lamarin. Wannan aikin da sojojin suka aikata sun saba wa ka’idojin aiki da ka’idojin hadin gwiwar hukumomin tsaro na kasa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Nasir Ya Naɗa Sabbin Sakatarori Na Ƙananan Hukumomi 21 A Kebbi

Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa

“Muna kira ga hukumomin da abin ya shafa da su dauki matakin gaggawa don magance wannan lamari tare da tabbatar da hukunta wadanda suka aikata laifin. Dole ne ‘yansanda da sojoji su hada kai don wanzar da zaman lafiya da tsaro a cikin al’umma.

“Hakazalika kada su yi tashe-tashen hankula da ke zubar da mutuncin jami’an tsaro ga idon jama’a.

“Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalai da abokan aikin SP Haliru Liman tare da tabbatar da cewa za mu yi duk mai yiwuwa don ganin an yi adalci wajen hukunta duk wanda aka sama da laifin kisan SP Haliru Liman DPO Wasagu a Jihar Kebbi.”

A karshen bayanin kisan gillar DPO Wasagu na kunshe ne a jawabin takardar manema labaru da jami’in hulda da jama’a na runduna Jihar Zamfara, ya sanya wa hannu, ASP Yazid Abubakar (Anipr) da aka raba wa manema labaru a Birnin Kebbi ta hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar Jihar Kebbi, SP Nafi’u Abubakar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaDPOKebbiKisaZamfaraZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Minista Ya Nemi A Ƙara Ƙulla Danƙon Zumunci A Tsakanin Nijeriya Da Kamfanin BBC

Next Post

‘Yansanda Sun Saki Durov, Zai Fuskanci Tuhume-tuhume A Faransa

Related

Gwamna Nasir Ya Naɗa Sabbin Sakatarori Na Ƙananan Hukumomi 21 A Kebbi
Labarai

Gwamna Nasir Ya Naɗa Sabbin Sakatarori Na Ƙananan Hukumomi 21 A Kebbi

3 hours ago
Kotu
Labarai

Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa

5 hours ago
Fahimtar Hakikanin kasar Sin
Labarai

Fahimtar Hakikanin kasar Sin

8 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara

8 hours ago
Iyalan Sarkin Da Aka Kama Suna Neman Taimakon Kudin Fanso Shi Miliyan ₦50
Tsaro

Iyalan Sarkin Da Aka Kama Suna Neman Taimakon Kudin Fanso Shi Miliyan ₦50

10 hours ago
Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Tsaro
Tsaro

Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Tsaro

11 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Saki Durov, Zai Fuskanci Tuhume-tuhume A Faransa

'Yansanda Sun Saki Durov, Zai Fuskanci Tuhume-tuhume A Faransa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Kai Wa Fararen Hula Da Kayayyakin More Rayuwa Hari A Sudan

Kasar Sin Na Adawa Da Kai Wa Fararen Hula Da Kayayyakin More Rayuwa Hari A Sudan

May 19, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Bunkasa Duk Da Matsaloli Da Dama

Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Bunkasa Duk Da Matsaloli Da Dama

May 19, 2025
Gwamna Nasir Ya Naɗa Sabbin Sakatarori Na Ƙananan Hukumomi 21 A Kebbi

Gwamna Nasir Ya Naɗa Sabbin Sakatarori Na Ƙananan Hukumomi 21 A Kebbi

May 19, 2025
Hadin Gwiwa Bisa Daidaito Da Girmama Juna Tsakanin Sin Da Amurka Zai Samar Da Moriyar Juna

Hadin Gwiwa Bisa Daidaito Da Girmama Juna Tsakanin Sin Da Amurka Zai Samar Da Moriyar Juna

May 19, 2025
Yankin Taiwan Ba Shi Da Iko Ko Hujjar Halartar Taron WHA

Yankin Taiwan Ba Shi Da Iko Ko Hujjar Halartar Taron WHA

May 19, 2025
Kotu

Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa

May 19, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Game Da Babban Shirin Shekaru Biyar-Biyar Na Bunkasa Tattalin Arziki Da Zamantakewar Kasar Sin Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Game Da Babban Shirin Shekaru Biyar-Biyar Na Bunkasa Tattalin Arziki Da Zamantakewar Kasar Sin Na 15

May 19, 2025
Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600

Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600

May 19, 2025
Gasar Wasanni Ta Kasa: FCT Ta Lallasa Borno Da Ci 4-1 A Wasan Farko

Gasar Wasanni Ta Kasa: FCT Ta Lallasa Borno Da Ci 4-1 A Wasan Farko

May 19, 2025
Fahimtar Hakikanin kasar Sin

Fahimtar Hakikanin kasar Sin

May 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.