ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Yi Allah-Wadai Da Kisan Gillar Da Sojoji Suka Yi Wa DPO Wasagu A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
'Yansanda

Rundunar ‘yansandan Jihar Zamfara, ta yi matukar bakin ciki da damuwa game da kisan gillar da aka yi wa Sufiritandan ‘Yansanda Haliru Liman, DPO a ofishin ‘yansanda a garin Wusagu, a Jihar Kebbi.

A ranar 28 ga watan Agusta, 2024, da misalin karfe 10:30 na safe, jami’an soji karkashin wani Hassan, da ke karkashin sashen Operation Hadain Daji, a unguwar Dan Marke a Bukkuyum, Jihar Zamfara, sun harbe SP Liman har lahira.

  • Minista Ya Nemi A Ƙara Ƙulla Danƙon Zumunci A Tsakanin Nijeriya Da Kamfanin BBC
  • Tawagar Jami’an Jihar Guangxi Ta Sin Ta Ziyarci Kasar Niger

Abubuwan da ke tattare da wannan lamarin suna da ban tsoro kuma ba za a yarda da su ba. SP Liman Haliru wanda ke kan hanyarsa ta halartar wani taro na wata-wata a Birnin Kebbi, jami’an soji ne suka tare shi duk da ya bayyana kansa a matsayin dan sanda.

ADVERTISEMENT

A wani yanayi mai ban tsoro da ya nuna, Hassan ya harbi SP Liman a kai, wanda ya yi sanadiyyar mutuwarsa nan take.

“Muna Allah-wadai da wannan kisan gillar bazata, muna kuma bukatar a gudanar da cikakken bincike a kan lamarin. Wannan aikin da sojojin suka aikata sun saba wa ka’idojin aiki da ka’idojin hadin gwiwar hukumomin tsaro na kasa.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

“Muna kira ga hukumomin da abin ya shafa da su dauki matakin gaggawa don magance wannan lamari tare da tabbatar da hukunta wadanda suka aikata laifin. Dole ne ‘yansanda da sojoji su hada kai don wanzar da zaman lafiya da tsaro a cikin al’umma.

“Hakazalika kada su yi tashe-tashen hankula da ke zubar da mutuncin jami’an tsaro ga idon jama’a.

“Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalai da abokan aikin SP Haliru Liman tare da tabbatar da cewa za mu yi duk mai yiwuwa don ganin an yi adalci wajen hukunta duk wanda aka sama da laifin kisan SP Haliru Liman DPO Wasagu a Jihar Kebbi.”

A karshen bayanin kisan gillar DPO Wasagu na kunshe ne a jawabin takardar manema labaru da jami’in hulda da jama’a na runduna Jihar Zamfara, ya sanya wa hannu, ASP Yazid Abubakar (Anipr) da aka raba wa manema labaru a Birnin Kebbi ta hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar Jihar Kebbi, SP Nafi’u Abubakar.

'Yansanda
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

MASU ALAKA

Auto Draft
Labarai

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
'Yansanda
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
'Yansanda
Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Saki Durov, Zai Fuskanci Tuhume-tuhume A Faransa

'Yansanda Sun Saki Durov, Zai Fuskanci Tuhume-tuhume A Faransa

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
'Yansanda

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
'Yansanda

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
'Yansanda

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.