• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙasar Sin Ta Ƙaddamar Da Ƙayataccen Shirin Bidiyo Na “Kwaɗon Baka” A Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ƙasar Sin Ta Ƙaddamar Da Ƙayataccen Shirin Bidiyo Na “Kwaɗon Baka” A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙasar Sin ta ƙaddamar da shirinta na bidiyo mai suna “Kwaɗon Baka” a Nijeriya, domin bunƙasa dangantaka a tsakanin Nijeriya da ƙasar Sin.
Kwaɗon baka shiri ne na bidiyo da ƙasar Sin take gabatarwa a harshen Hausa da ke nuna al’adunta da kayayyakin tarihi da kaɗe-kaɗe da raye-raye domin ilmantar da al’ummar duniya a harshen Hausa.
Bikin ya gudana ne a cibiyar ƙasar Sin da ke Babbar Birnin Tarayya Abuja, wanda ya samu halartar ɗimbin baƙi na cikin gida Nijeriya da kuma ƙasar Sin.
An ƙaddamar da aikin ɗaukar shirin bidiyon kwaɗon baka bisa haɗin gwiwa a tsakanin rukunin kafafen yaɗa labarai na ƙasar Sin (CMG) da kuma gidan talabijin na ƙasa (NTA).

Shiri
Da yake gabatar da jawabi wajen ƙaddamarwar, ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed idris ya bayyana cewa ya yi farin cikin halartar wannan biki na gabatar da wannan shirin wanda haɗin gwiwa ne tsakanin NTA da CMG na China.
Ministan wanda ya samu wakilcin daraktan ma’aikatar yaɗa labarai, Dakta Sulaiman Haruna, ya ƙara da cewa haƙiƙa wannan shiri zai ƙara inganta dangantaka tsakanin tashosin talbijin na Nijeriya da rukunin kafafen yaɗa labarai na ƙasar Sin, kuma wannan wani ɓangare ne na jaddada hulɗar dangataka tsakanin al’ummar Nijeriya da ƙasar Sin, ta fuskar yaɗa al’adu da harsunan ƙasashen biyu, da sauran kafafen sadarwa na zamani da ke ƙasashen.

Shiri
A cewarsa, gidajen yaɗa labarai na taka muhimmiyar rawa wajen sanya al’umma bisa hanya madaidaiciya, domin kawo fahimtar juna da samar da ingantaccen ci gaba, saboda haka ya ce gidajen yaɗa labarai na da kyakkyawar rawar da za su taka wajen ƙara inganta harkar zamantakewa, ci gaban tattalin arzikin ƙasa da bunƙasa al’adu da ke buƙatar ganin an sanar da mutane.
“Ina mai jinjina ga hukumomin watsa labarai na Sin da kuma hukumar talibijin ta ƙasa (NTA), saboda rawar da suke takawa wajen samar da sahihan labarai da shirye-shirye masu ma’ana da suke gabatarwa domin ci gaban ƙasashen biyu.
“Akwai buƙatar daidaito a wajen ba da labarai, musanman wajen faɗin irin ci gaba da nasarorin da ƙasar nan ta samu da kuma samar da shirye-shirye da za su ƙara wa masu tasowa kyakkyawan fata nan gaba.

Shiri

“Nijeriya tana da matasa masu himma da ke ƙoƙarin aiki tukuru wajen ganin sun yi amfani da damarsu duk da irin ƙalubalen da suke fuskanta. Wasu daga cikin manyan ƙalubalen da matasa ke fuskanta a ƙasar nan da sauran ƙasashen duniya shi ne, yadda ake samun yaɗuwar labaran ƙanzon kurege da jita-jita da labaran ƙarya wanda ya kawo koma-baya da kuma rashin yarda tsakanin gwamnati da al’umarta.
“Yana da muhimmanci ga kafofin yaɗa labarai na ƙasar Sin su taimaka wajen magance wannan matsala ta hanyar yin aiki tare da sauran takwarorinsu na ƙasashen duniya domin su kawo ƙarshen wannan mummunar ɗabi’a da tabbatar da cewa kafafen yaɗa labarai sun ci gaba da zama abin dogaro da nuna sanin ya kamata.
“Akwai buƙatar ƙasar Sin ta ƙara faɗaɗa tashohinta a Nijeriya ta hanyar ƙara sanya wasu harsuna da suka haɗa da Hausa da Igbo da Yoruba da Pidgin domin isar da saƙonni da samar da ayyukan yi da horas da ‘yan Nijeriya.” In ji ministan.
A nasa jawabin, babban jami’in kula da ɓangaren al’adu na ofishin jakadancin ƙasar Sin da ke Nijeriya, Li Xuda ya bayyana cewa Nijeriya da ƙasar Sin suna da daɗaɗɗiyar hulɗa ta hanyar bunƙasa al’adu da tattalin arziki da da dai sauran fannoni masu yawan gaske.
Ya ce a farkon shekara ta 2022, an yi ganawa a tsakanin Nijeriya da Sin ta ɓangaren al’adu da harkokin yawon buɗe ido, wanda aka tattauna kan nasarorin da ƙasashen biyu suka samu a ɓangaren al’adu da yawon buɗe ido, sannan an amince a ci gaba da hulɗar bunƙasa al’adu a tsakanin ƙasashen biyu.

Labarai Masu Nasaba

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shiri
Har ila yau, mataimakiyar shugaban sashin Hausa na CMG, Kande Gao ta ce ƙaddamar da wannan shirin a Nijeriya ya zama wani gagarimin biki wurinta da kuma al’ummar ƙasar Sin.
Ta ƙara da cewa, bisa binciken da suka gudanar, wannan shiri ya samu matuƙar amsuwa, musamman a Nijeriya da sauran ƙasashen Afirka, inda hakan ta ƙara ba su ƙwarin gwiwa wajen ci gaba da aiwatar da ayyukan da suke yi.

Shiri
Shi kuwa a nashi ɓangaren, shugaban gidan talabijin na NTA, Malam Salihu A. Dembos ya ce wannan ba ƙaramin abin alfari ba ne a ce ƙasar Sin ta ƙaddamar da shirinta a Nijeriya.
Shugaban na NTA wanda shugaban sashin Hausa na NTA, Aminu Isiyaka Abbas ya wakilta, ya ce lallai za su yi duk wani abu mai yiwuwa wajen bunƙasa wannan alaƙa ta al’ada a tsakanin Nijeriya da ƙasar Sin.
Daga cikin abubuwan da suka ƙayatar a wurin bikin ƙaddamar da shirin na Kwadon Baka dai har da nuna wasu wasanni na al’adun Sinawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaBidiyoHadin GwiwaKawanceKwadon BakaLabaraiNijeriyaShiriSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Afrika Sun Samu Ci Gaba Mai Armashi Wajen Aiwatar Da Shawarar BRI

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa ‘Yan Kasuwa Wata Guda Su Sauke Farashin Kayayyakin Masarufi

Related

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
Daga Birnin Sin

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

16 minutes ago
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

17 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

18 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

19 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

20 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

21 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa ‘Yan Kasuwa Wata Guda Su Sauke Farashin Kayayyakin Masarufi

Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa ‘Yan Kasuwa Wata Guda Su Sauke Farashin Kayayyakin Masarufi

LABARAI MASU NASABA

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.