• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Karfafa Kawance Da Bunkasa Damammakin Hadin Gwiwa

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Karfafa Kawance Da Bunkasa Damammakin Hadin Gwiwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nan da ’yan kwanaki kalilan, shugabannin Sin da na kasashen Afirka za su sake haduwa a birnin Beijing, inda ake sa ran sake sabunta kawance, da tattauna tsare-tsaren bunkasa hadin gwiwa. Masharhanta na ganin wannan taro zai share fagen zurfafa amincewa da juna, da daga martabar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka, tare da karfafa rungumar manufofi da sassan biyu suka amincewa, ta yadda za a kai ga gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya bisa matsayin koli.

 

Idan mun yi la’akari da matakai daban daban da bangaren Sin ke dauka, musamman yadda shugaban kasar Xi Jinping ke dora muhimmancin gaske ga hadin gwiwar Sin da Afirka, ta hanyar fitar da tsare-tsare na raya kawancen su, da gabatar da manufofin cimma nasarori daki-daki, ma iya cewa Sin da Afirka na tunkarar wata makoma mai haske ta cimma manyan nasarori yadda ya kamata.

  • Ƙasar Sin Ta Ƙaddamar Da Ƙayataccen Shirin Bidiyo Na “Kwaɗon Baka” A Nijeriya
  • Sin Da Afirka Aminai Ne Wajen Neman Zamanantar Da Kansu

Idan mun waiwayi baya, muna iya tuna ziyarar da shugaba Xi ya gudanar a nahiyar Afirka a watan Maris na shekarar 2013, inda ya gabatar da wasu manufofi masu nasaba da bunkasa alakar Sin da nahiyar Afirka. Kana a yayin taron dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, wanda ya gudana a birnin Johannesburg na Afirka ta kudu a watan Disambar 2015, shugaban na Sin ya bayyana shirin aiwatar da wasu manyan manufofin hadin gwiwa da Afirka har guda 10, kana sassan biyu suka amince da daga matsayin kawancensu zuwa dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare daga dukkanin fannoni. Kuma shekaru 3 bayan hakan a shekarar 2018, shugaban na Sin ya karbi bakuncin taron FOCAC na birnin Beijing, inda ya ayyana manufar nan ta kara kusantar juna tsakanin Sin da kasashen Afirka don kaiwa ga gina al’ummar sassan biyu mai makomar bai daya a sabon zamani.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Dukkanin wadannan da wasu makamantansu da dama, matakai ne dake nuna yadda har kullum Sin ke nacewa burin cimma nasarar hadin gwiwa da kasashen Afirka.

 

Yayin da kasashe masu tasowa ke kara fahimtar muhimmancin tafiya tare, Sin da kasashen Afirka na kara ingiza hadin kai da cimma moriya tare, lamarin dake zama wani karfi na kafuwar duniya mai makomar bai daya, wadda za ta amfani daukacin al’ummunta ta fuskar raya tattalin arziki da zamantakewa, da dunkulewa guri guda, kamar dai yadda a ko da yaushe taron dandalin FOCAC ke kara ingiza wannan manufa.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Luwaɗi Da Maɗigo: Gwamnatin Bauchi Ta Gayyaci Sheikh Gadon-Kaya Don Ƙarin Haske

Next Post

Adadin Masu Amfani Da Intanet A Kasar Sin Ya Kai Biliyan 1.1

Related

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam
Daga Birnin Sin

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

9 hours ago
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

10 hours ago
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

11 hours ago
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

12 hours ago
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

13 hours ago
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

14 hours ago
Next Post
Adadin Masu Amfani Da Intanet A Kasar Sin Ya Kai Biliyan 1.1

Adadin Masu Amfani Da Intanet A Kasar Sin Ya Kai Biliyan 1.1

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.