• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Tsare-tsaren Gwamnatin Tarayya Guda 11

by Adamu Rabiu
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Batun Tsare-tsaren Gwamnatin Tarayya Guda 11
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan faduwar ba zato ba tsammani biyo bayan cire tallafin man fetur, gwamnatin yanzu da ta mamaye Aso-Rock, a tsarin da ya yi kama da mai neman gudunmawar kashe gobara, ta yanke shawarar kaddamar da shiri daya bayan daya wanda muke fatan zai inganta rayuwar ‘yan Nijeriya a bangarori daban-daban. Wadannan shirye-shiryen, sun hada da raba abubuwan jin dadi, raba shinkafa, tallafin kudi, zuwa damar samun rancen kudi, zuwa horo da sauransu.

Amma kamar kowane shiri na wannan gwamnatin, su zo da nasu fa’idoji da abubuwan da zasu iya haifar da koma baya.

  • ‘Yan Majalisar Tarayya 29 Da Suka Mutu A Kan Kujerunsu Cikin Shekara 9
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa ‘Yan Kasuwa Wata Guda Su Sauke Farashin Kayayyakin Masarufi

Anan za mu binciki guda 11 don sanin ko suna nuni ne da sadaukar war gwamnati ko labulen taga ce ko kuma rudu ne kawai?

Bari Mu Nutse Cikin Shirye-Shiryen Guda 11

Tsarin Lamunin Dalibai:

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Asusun ba da Lamuni na Ilimi na Nijeriya (NELFUND) yana samun kudade ne daga Hadaddiyar Asusun Gwammnatin Tarayya da kuma kudin da aka kwato daga hannun azzaluman kasa.

Shirin na nufin bayar da lamuni marar riba ga daliban da ke neman ilimin jami’a. Wannan shiri dai ya samo asali ne daga sashe na 18 na kundin tsarin mulkin Nijeriya, wanda ya samar da damammakin samun ilimi na boko da kuma na yau da kullun a matsayin hanyar karfafawa ‘yan kasa da bunkasa ci gaban kasa.

A matsayin mafita ga dalibai, zai yi kyau a ziyar ci shafin- http://nelf.gob.ng

Shirin CNG na Shugaban kasa: Wannan canjin fasalin motoci zuwa anfani da iskar Gas (CNG) ne, anan gwamnati ta yi niyyar zuwa rancen kudi dalar amurka USD250m (daidai da NGN397.5b). Ma’aikatar Kudi, da na Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari, da na Albarkatun Man Fetur, da Ma’aikatar kwadago, da na Sufuri ne za su gudanar da shirin.

Shirin na neman inganta amfani da iskar gas a matsayin mai tsabta, mafi araha maimakon man fetur. Wannan ya yi dai-dai da kundin tsarin mulki na samun yanayi mai kyau a karkashin sashe na 20.

Tsarin zai yi canjin kyauta ga membobin kungiyoyin sufuri da yanke farashin kashi 50% ga masu aikin abun hawa na haya (wato ride-share a turance). Domin cin gajiya, sai a ziyarci shafin https://pci.gob.ng

Wani hanzari, mene ne makomar wadanda ba su cikin wannan rukuni na cancanta?

Kamfanin Ba Da Lamuni ga Ma’aikata: Hukumar ba da lamuni ta Nijeriya (CrediCorp) na karkashin ma’aikatar kudi ta tarayya kuma tana da niyyar kiwon kusan ma’aikata miliyan 40 na gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu don su kara yawan amfanin da bashi domin bunkasa sayan abun masarufi na yau da kullun. Sashi na 16 na kundin tsarin mulkin Nijeriya, ya umurci gwamnati ta inganta tattalin arzikin dukkan ‘yan kasa.

A matsayin shirin da zai haifar da inganta rayuwar ‘yan Nijeriya, zai dace a ziyarci shafin https://credicorp.ng

Sai dai abin mamaki a nan shi ne, su kuma sauran ‘yan Nijeriya miliyan 180 da suka rage wa’anda basu aikin gwamnati ko aikin blue-collar mece ce makomar su a cikin wannan tsari?

Shirin Kamfanoni na Dijital da Kirkire-Kirkire (iDiCE): Shirin wanda Bankin masana’antu ke gudanarwa, yana tallafawa ‘yan kasuwa na dijital da kere-kere da kudade da albarkatu, yana baiwa matasa damar yin amfani da basirarsu. Yana da goyon bayan sashe na 17 na kundin tsarin mulkin Nijeriya, wanda ya ba da umarnin tabbatar da adalci na zamantakewa, inganta rayuwar ‘yan kasa, da magance matsalolin da suka shafi kiwon lafiya, ilimi, da jin dadin jama’a.

Saboda shirin ya kunshi lamuni zai kyautatu a ziyarci shafin- https://boi.ng/iDiCE

Shirin Inganta Kwaraiwar masu Aiki (SUPA): Hakkin gudanarwan ya na hanun asusun horar da ma’aikatan masana’antu (ITF) ne. Shirin yana mai da hankali kan habaka kwarewar masu sana’a, ta yadda za a habaka dogaro da kai da kasuwanci. Sashi na 16 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya yi kira da a samar da ci gaban kasa.

A ziyaraci shafin https://SUPA.itf.gob.ng domin cin gajiyan shirin.

Zauren Koyar da Matasan Nijeriya (NIYA): Ma’aikatar Matasa da Wasanni ta Tarayya ne za ta gudanar da shi, kuma za ta hada da nasiha da horar da matasan Nijeriya. Hakan ya yi daidai da sashe na 17 na kundin tsarin mulkin Nijeriya wanda ya wajabta wa gwamnati tabbatar da ci gaban matasa.

Ziyartan shafin https://NIYA.ng zai dace don ganin abubuwan da su kace za su yi.

Shirin Fitar da Hazakar Matasa na Kasa (NATEP): Ma’aikatar masana’antu, kasuwanci da zuba jari za ta gudanar da wannan shirin. Kuma a zahiri, ya kunshi horo. Shirin na nufin fitar da hazakar matasan Nijeriya a fagen wasanni, fasaha da al’adu zuwa kasashen waje. Shirin ya yi daidai da sashe na 17, manufofin zamantakewa na kundin tsarin mulkin Nijeriya, wanda ya ba da umarnin tabbatar da adalci na zamantakewa, inganta rayuwar jama’a, da raya al’adu da dai sauransu.

Ga wadanda ke son yin JAPA, ziyartar shafin http://natep.gob.ng ya zama tilas.

Shirin Bada Lamuni ga Kananan ‘yan Kasuwa: Wannan tsarin Bankin Masana’antu ne za ta gudanar,kuma zai ba da taimako na kudi ga kananan ‘yan kasuwa. Zai kuma karfafa ci gaban tattalin arziki da kuma samar da aiki. Sashe na 16, makasudin tattalin arziki, na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ta goyi bayan wannan tsarin, inda ta tabarta da rarraba wadata, da walwala daidai tsakanin ‘ yan kasa domin samun kwanciyar hankali.

Ziyartar shafin https://boi.ng/micro-business ya dace a wannan gabar.

Tsarin Ba da Lamuni na Sayen Gida ko Matsuguni: Hukumar Kula da Gidaje ta Tarayya (FHA) ce ke kula da wannan. Manufar ita ce samar da gidaje masu rahusa ga ‘yan Nijeriya, tare da tallafawa. Kowane dan Nijeriya na da hakkin samun isasshen matsuguni kamar yadda yake kunshe a cikin sashe na 16, manufofin tattalin arziki, na kundin tsarin mulkin Nijeriya, ya jaddada daidaiton wajen rarraba dukiya da albarkatun kasa a tsakanin ‘yan kasa.

Yayin da shirin ke magance wata muhimmiyar bukata, shirin na ma’aikata ne masu asusun ajiyar siyan gidaje kawai (wato National Housing Fund).

Abun tambaya a nan, mece ce makomar ‘yan Nijeriya da ba su da aikin yi? Shin gidajen suna da araha kuma suna da inganci? Shafin http://fha.gob.ng/ongoing-projects ya bada karin bayani.

Tsarin Koyarwa da Horarwa ta NDDC: Wannan tsarin yana ba da horo da tallafi ga matasa da suka kammala karatun digiri a yankin Neja Delta, tare da habaka kwarewa a aiki. Ya yi daidai da sashe na 17, manufofin zamantakewa na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya wanda ya nuna sadaukar da kai da adalci na zamantakewa, inganta yanayin rayuwa ga ‘yan kasa da dai sauransu. To amma, shin shirin yana fuskantar tsoma bakin ‘yan siyasa da cin hanci da rashawa? A ziyarci shafin https://nyis.nddc.gob.ng domin Karin bayani.

Tallafin kudi da lamuni ga kanana ‘yan Kasuwa: Shirin Tallafawan (wato Nano-Business Support) yana karkashin kulawar ma’aikatar masana’antu, kasuwanci da zuba jari ta tarayya, ya kasu kashi biyu, yana bayar da tallafin kudi ga kananan ‘yan kasuwa ta hanyar ba su naira dubu hamsin kowanne, yayin da a daya bangaren kuma akwai lamuni wanda ake ba ‘yan kasuwa. Manufar ita ce a taimaka musu su ci gaba da ba da gudummawa ga tattalin arziki. Wannan ya yi daidai da manufar sashe na 16 na kundin tsarin mulkin Nijeriya wanda ya jaddada daidaiton rabon dukiya da albarkatu a tsakanin ‘yan kasa.

Babban kalubale a nan shi ne cewa zababbun wakilanku dole ne su sani kuma su shigarda sunaye a cikin jerin wadanda za su amfana tun tashin farko. Lalle wannan tsarin abun tunani ne!

A ziyarci shafin https://fedgrantandloan.gob.ng domin fahintar kofar ragon da aka shirya a tsarin.

Hakikanin Gaskiyar Al’amuran Nijeriya

Wannan ababen su ne abin da muke gani na faruwa ga shirye-shiryen guda 11:

Matsalolin Kudi – Duk wadannan shirye-shiryen suna bukatar kudi masu yawa. Rashin kudi da kuma tekun bashin da Nijeriya ke ciki babban kalubale ne ga aiwatar da shirye-shiryen.

Cin hanci da rashawa da almundahana -Wannan babban kalubale ne a Nijeriya. Batun almubazzaranci da kudaden gwamnati da rashin gaskiya su ne al’amuran da ake fuskanta yau da kullum.

Rashin Fadakarwa da Wayar da Kai -Shin akwai yuwuwar wadannan shirye-shiryen za su kai ga wadanda za su ci gajiyar shirin saboda rashin isassun kafen wayar da kan jama’a ko wahalhalun da ake samu wajen kaiwa ga wurare masu nisa? Fatan wannan rahoton shine taimakawa wajen yada wadannan shirye-shiryen daban-daban don isa ga wadanda zasu ci gajiyar shirin.

Karancin ababen more rayuwa – Rashin isassun kayayyakin more rayuwa kamar samar da wutar lantarki, sufuri, da sadarwa na iya shafar isar da shirye-shiryen da sa ido. Tuni matsalar kawar da tallafin wutar lantarki na shafar nasarar tsare-tsaren.

Kwarewar masu gudanar da shirye-shiryen na da alamun tambaya kuma kalubale ne.

Yiwuwar Dorewa da Tasirin Tsare-tsaren na Tsawon Lokaci – Masu gudanar da shirin suna bukatar nuna tasirin shirin na dogon lokaci da dorewa fiye da aiwatarwa da shirin a matakin farko ba hayaniya ba maras amfani.

Hadin kai Tsakanin Masu Ruwa da Tsaki – Shin akwai hadin gwiwa mai inganci tsakanin hukumomin gwamnati, kungiyoyin sa-kai, da abokan hulda masu zaman kansu?

Tattara bayanai da Kulawa – Samar da ingantattun hanyoyin tattara bayanai da hanyoyin sa ido suna da mahimmanci don tantance tasirin shirin da yanke shawara mai inganci.

Burinmu

Jama’a ka da su yi shakkar yin amfani da wadannan damammaki. Kundin tsarin mulkin Nijeriya ya ba da tabbacin samar da ginshikin doka ga duk ‘yan kasa don cin gajiyar wadannan shirye-shirye.

Idan akwai batutuwan da suka shafi biyan bashin, Sashe na 42 na kundin tsarin mulki na iya zama kariya ta hanyar tabbatar da cewa babu wani dan kasa da ake nuna masa wariya bisa rashin ka’ida a cikin gudanarwa ko aiwatar da hanyoyin biyan basussukan.

A karshe, a matsayinmu na ’yan Nijeriya, bai kamata mu yi kasa a gwiwa ba na dagewa a kan tabbatar da aiwatar da aikin gwamnati cikin gaskiya da rikon amana.

Tsari da adalci da ta fi dacewa ga duk ’yan Nijeriya abu ne mai yiwuwa nan gaba ba da jimawa ba!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: TallafiTarayya
ShareTweetSendShare
Previous Post

ACF Ta Yaba Wa Tinubu Kan Amincewa Da Ziyarar Sulhu Da Shugaban Sojojin Nijeriya Ya Kai A Nijar 

Next Post

Da Ɗumi-ɗumi: Gobara Ta Tashi A Gidan Gwamnatin Katsina

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

2 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

4 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

6 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

7 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

7 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

12 hours ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: Gobara Ta Tashi A Gidan Gwamnatin Katsina

Da Ɗumi-ɗumi: Gobara Ta Tashi A Gidan Gwamnatin Katsina

LABARAI MASU NASABA

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.