• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Afirka: FOCAC Ya Zama Abun Misali Mai Kyau Ga Inganta Hadin-Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Afirka: FOCAC Ya Zama Abun Misali Mai Kyau Ga Inganta Hadin-Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi bikin bude taron kolin dandalin FOCAC, wato dandalin tattauna hadin-kan Sin da Afirka da safiyar yau Alhamis 5 ga watan Satumba, a babban dakin taron al’umma dake Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

 

Shugaban kasar Senegal dake jagorantar dandalin FOCAC tare da kasar Sin, Bassirou Diomaye Faye, da shugaban kasar Mauritaniya dake jagorantar kungiyar tarayyar Afirka (AU) a wannan zagaye, Mohamed Ould Cheikh Mohamed Ahmed Ghazouani, da shugaban kasar Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, da shugaban tarayyar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, da shugabar kasar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan, sun gabatar da muhimman jawabai a wajen bikin.

  • An Zartas Da Sanarwar Beijing Da Tsarin Aiki A Taron FOCAC
  • An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

Shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, FOCAC ba dandali da kadai ya taka rawa wajen habaka dangantakar abokantaka tsakanin Afirka da Sin ba ne, har ma ya zama wani kyakkyawan abun misali ta fuskar jagorantar hadin-gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Ana gudanar da hadin-gwiwar ne daidai bisa sada zumunta, da girmama juna, tare da cimma moriyar juna, kuma kasar Sin na hada kai tare da kasashen Afirka ba tare da gindaya wani sharadin siyasa ba, al’amarin da ya taimaka sosai ga karfafa tuntuba da mu’amalar juna, da habakar tattalin arziki, da kyautatar rayuwar dan Adam a kasashen Afirka. A yanayi mai sarkakkiyar da ake ciki, zurfafa hadin-gwiwa tare da kasar Sin, yana samar da kyakkyawan fata ga kasashen Afirka, na cimma burikan wanzar da zaman lafiya, da zaman karko, da samar da ci gaba mai dorewa.

 

Labarai Masu Nasaba

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Shugabannin Afirka sun kuma yaba sosai, tare da nuna cikakken goyon-baya ga muhimmin ra’ayin da shugaba Xi Jinping ya bullo da shi, wato ra’ayin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya, da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, da sauran wasu shawarwarin da suka shafi samar da ci gaba, da tabbatar da tsaro, da raya wayewar kai a duk fadin duniya. Sun ce suna tsayawa tsayin daka kan manufar Sin daya tak a duniya, da marawa gwamnatin kasar Sin baya wajen kokarin dunkule duk kasa baki daya, da nuna adawa da duk wani yunkuri da aka yi na tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin ta hanyar fakewa da batutuwan da suka shafi Taiwan da hakkin dan Adam.

 

Kaza lika, shugabannin kasashen Afirka suna da yakinin cewa, zurfafa yin gyare-gyare a gida daga dukkan fannoni, gami da kara zamanantar da kasa da kasar Sin take yi, zai kara samar da damammakin ci gaba ga kasa da kasa, ciki har da kasashen Afirka.

 

Kasashen Afirka suna fatan aiwatar da nasarorin taron kolin na wannan karo a zahiri, da taimakawa ci gaban sana’o’in zamani, da zamanantar da ayyukan noma, da gina al’ummomin Sin da Afirka bisa kyakkyawar makoma ta bai daya a sabon zamanin da muke ciki, don kirkiro makoma ta zaman lafiya da kwanciyar hankali, da zaman wadata da kuma ci gaba. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Peng Liyuan Ta Halarci Taron Karawa Juna Sani Game Da Raya Ilimi Na Sin Da Afirka Tare Da Matan Shugabannin Afirka

Next Post

Tsadar Sufuri: Jihar Kwara Ta Kaddamar Da Sufuri Kyauta

Related

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo
Daga Birnin Sin

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

14 hours ago
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta
Daga Birnin Sin

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

15 hours ago
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

16 hours ago
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

18 hours ago
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan
Daga Birnin Sin

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

19 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

2 days ago
Next Post
Tsadar Sufuri: Jihar Kwara Ta Kaddamar Da Sufuri Kyauta

Tsadar Sufuri: Jihar Kwara Ta Kaddamar Da Sufuri Kyauta

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

September 8, 2025
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.