ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Afirka: FOCAC Ya Zama Abun Misali Mai Kyau Ga Inganta Hadin-Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
FOCAC

An yi bikin bude taron kolin dandalin FOCAC, wato dandalin tattauna hadin-kan Sin da Afirka da safiyar yau Alhamis 5 ga watan Satumba, a babban dakin taron al’umma dake Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

 

Shugaban kasar Senegal dake jagorantar dandalin FOCAC tare da kasar Sin, Bassirou Diomaye Faye, da shugaban kasar Mauritaniya dake jagorantar kungiyar tarayyar Afirka (AU) a wannan zagaye, Mohamed Ould Cheikh Mohamed Ahmed Ghazouani, da shugaban kasar Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, da shugaban tarayyar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, da shugabar kasar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan, sun gabatar da muhimman jawabai a wajen bikin.

ADVERTISEMENT
  • An Zartas Da Sanarwar Beijing Da Tsarin Aiki A Taron FOCAC
  • An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

Shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, FOCAC ba dandali da kadai ya taka rawa wajen habaka dangantakar abokantaka tsakanin Afirka da Sin ba ne, har ma ya zama wani kyakkyawan abun misali ta fuskar jagorantar hadin-gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Ana gudanar da hadin-gwiwar ne daidai bisa sada zumunta, da girmama juna, tare da cimma moriyar juna, kuma kasar Sin na hada kai tare da kasashen Afirka ba tare da gindaya wani sharadin siyasa ba, al’amarin da ya taimaka sosai ga karfafa tuntuba da mu’amalar juna, da habakar tattalin arziki, da kyautatar rayuwar dan Adam a kasashen Afirka. A yanayi mai sarkakkiyar da ake ciki, zurfafa hadin-gwiwa tare da kasar Sin, yana samar da kyakkyawan fata ga kasashen Afirka, na cimma burikan wanzar da zaman lafiya, da zaman karko, da samar da ci gaba mai dorewa.

 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Shugabannin Afirka sun kuma yaba sosai, tare da nuna cikakken goyon-baya ga muhimmin ra’ayin da shugaba Xi Jinping ya bullo da shi, wato ra’ayin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya, da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, da sauran wasu shawarwarin da suka shafi samar da ci gaba, da tabbatar da tsaro, da raya wayewar kai a duk fadin duniya. Sun ce suna tsayawa tsayin daka kan manufar Sin daya tak a duniya, da marawa gwamnatin kasar Sin baya wajen kokarin dunkule duk kasa baki daya, da nuna adawa da duk wani yunkuri da aka yi na tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin ta hanyar fakewa da batutuwan da suka shafi Taiwan da hakkin dan Adam.

 

Kaza lika, shugabannin kasashen Afirka suna da yakinin cewa, zurfafa yin gyare-gyare a gida daga dukkan fannoni, gami da kara zamanantar da kasa da kasar Sin take yi, zai kara samar da damammakin ci gaba ga kasa da kasa, ciki har da kasashen Afirka.

 

Kasashen Afirka suna fatan aiwatar da nasarorin taron kolin na wannan karo a zahiri, da taimakawa ci gaban sana’o’in zamani, da zamanantar da ayyukan noma, da gina al’ummomin Sin da Afirka bisa kyakkyawar makoma ta bai daya a sabon zamanin da muke ciki, don kirkiro makoma ta zaman lafiya da kwanciyar hankali, da zaman wadata da kuma ci gaba. (Murtala Zhang)

FOCAC
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
FOCAC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Tsadar Sufuri: Jihar Kwara Ta Kaddamar Da Sufuri Kyauta

Tsadar Sufuri: Jihar Kwara Ta Kaddamar Da Sufuri Kyauta

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.