ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Afirka: FOCAC Ya Zama Abun Misali Mai Kyau Ga Inganta Hadin-Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
FOCAC

An yi bikin bude taron kolin dandalin FOCAC, wato dandalin tattauna hadin-kan Sin da Afirka da safiyar yau Alhamis 5 ga watan Satumba, a babban dakin taron al’umma dake Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

 

Shugaban kasar Senegal dake jagorantar dandalin FOCAC tare da kasar Sin, Bassirou Diomaye Faye, da shugaban kasar Mauritaniya dake jagorantar kungiyar tarayyar Afirka (AU) a wannan zagaye, Mohamed Ould Cheikh Mohamed Ahmed Ghazouani, da shugaban kasar Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, da shugaban tarayyar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, da shugabar kasar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan, sun gabatar da muhimman jawabai a wajen bikin.

ADVERTISEMENT
  • An Zartas Da Sanarwar Beijing Da Tsarin Aiki A Taron FOCAC
  • An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

Shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, FOCAC ba dandali da kadai ya taka rawa wajen habaka dangantakar abokantaka tsakanin Afirka da Sin ba ne, har ma ya zama wani kyakkyawan abun misali ta fuskar jagorantar hadin-gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Ana gudanar da hadin-gwiwar ne daidai bisa sada zumunta, da girmama juna, tare da cimma moriyar juna, kuma kasar Sin na hada kai tare da kasashen Afirka ba tare da gindaya wani sharadin siyasa ba, al’amarin da ya taimaka sosai ga karfafa tuntuba da mu’amalar juna, da habakar tattalin arziki, da kyautatar rayuwar dan Adam a kasashen Afirka. A yanayi mai sarkakkiyar da ake ciki, zurfafa hadin-gwiwa tare da kasar Sin, yana samar da kyakkyawan fata ga kasashen Afirka, na cimma burikan wanzar da zaman lafiya, da zaman karko, da samar da ci gaba mai dorewa.

 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Shugabannin Afirka sun kuma yaba sosai, tare da nuna cikakken goyon-baya ga muhimmin ra’ayin da shugaba Xi Jinping ya bullo da shi, wato ra’ayin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya, da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, da sauran wasu shawarwarin da suka shafi samar da ci gaba, da tabbatar da tsaro, da raya wayewar kai a duk fadin duniya. Sun ce suna tsayawa tsayin daka kan manufar Sin daya tak a duniya, da marawa gwamnatin kasar Sin baya wajen kokarin dunkule duk kasa baki daya, da nuna adawa da duk wani yunkuri da aka yi na tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin ta hanyar fakewa da batutuwan da suka shafi Taiwan da hakkin dan Adam.

 

Kaza lika, shugabannin kasashen Afirka suna da yakinin cewa, zurfafa yin gyare-gyare a gida daga dukkan fannoni, gami da kara zamanantar da kasa da kasar Sin take yi, zai kara samar da damammakin ci gaba ga kasa da kasa, ciki har da kasashen Afirka.

 

Kasashen Afirka suna fatan aiwatar da nasarorin taron kolin na wannan karo a zahiri, da taimakawa ci gaban sana’o’in zamani, da zamanantar da ayyukan noma, da gina al’ummomin Sin da Afirka bisa kyakkyawar makoma ta bai daya a sabon zamanin da muke ciki, don kirkiro makoma ta zaman lafiya da kwanciyar hankali, da zaman wadata da kuma ci gaba. (Murtala Zhang)

FOCAC
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
FOCAC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Tsadar Sufuri: Jihar Kwara Ta Kaddamar Da Sufuri Kyauta

Tsadar Sufuri: Jihar Kwara Ta Kaddamar Da Sufuri Kyauta

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.