• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fashewar Tankar Mai: Minista Ya Jajanta Wa Al’ummar Neja Da Iyalan Mutum 59 Da Suka Mutu

by Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Yajin aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, a ranar Litinin ya jajanta wa al’ummar Jihar Neja bisa rasuwar mutane 59 a wani haɗarin mota da ya ritsa da su a hanyar Bida-Agaie-Lapai ranar Lahadi.

 

A cikin saƙon ta’aziyya da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim, ya sanya wa hannu, ya ce, lamarin ya girgiza Jihar Neja da ƙasa baki ɗaya.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Tankar Mai Ta Fashe Ta Kashe Mutane 30 A Neja
  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Kungiyar Kasashen Musulmi A Bangarori Daban-Daban

Ya yi addu’ar Allah ya ba iyalan mamatan ikon jure wannan babban rashin.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

Idris ya ce: “Ina miƙa ta’aziyya ta ga gwamnati da al’ummar Jihar Neja da iyalai, abokai da ‘yan’uwan mutane 48 da suka rasa rayukan su a wani mummunan hatsari da ya auku a hanyar Bida-Agaie-Lapai a Jihar Neja da sanyin safiyar Lahadi, 8 ga Satumba, 2024.

 

“Wannan mummunan lamari ya girgiza ɗaukacin Jihar Neja da ma ƙasa baki ɗaya kuma ina yi wa duk waɗanda abin ya shafa a wannan lokaci mai zafi addu’a. Don haka ina taya al’ummar Jihar Neja da ma Nijeriya baki ɗaya alhinin wannan babban rashi.

 

“Allah ya jiƙan waɗanda suka rasu kuma Allah ya bai wa iyalan su juriyar wannan rashi mara misaltuwa.”

 

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC), reshen Jihar Neja, Mista Kumar Tsukwan, ya shaida wa manema labarai a ranar Litinin cewa dukkan waɗanda abin ya shafa maza ne, kuma da ba a iya tantance motocin da abin ya shafa ba saboda tsananin ƙonewar su.

 

Tsukwan ya bayyana cewa lambar mota ɗaya kacal ce aka iya tantancewa, yayin da ba a gane lambobin sauran ba.

Ya ƙara da cewa lamarin ya faru ne da ƙarfe 4:30 na safe kuma an kai rahoton lamarin ga sashin Lapai na FRSC da ƙarfe 4:40 na safe.

 

Ya ce: “Motar tankar man da ke ɗauke da mai daga Legas zuwa Kano tana gudu sosai, inda ta ƙwace ta faɗi ta kama da wuta yayin da wutar ta shafi wata tirela da ke ɗauke da shanu da mutane tare da wasu motoci biyu a baya. Dukkan motocin guda huɗu sun ƙone ƙurmus.”

“An ruwaito cewa sai da ɗaya daga cikin fasinjojin tirelar da ke ɗauke da mutane da shanun ya ankarar da direban cewa akwai wuta fa a gaban su amma sai direban ya amsa da cewa taya ce kawai ke ƙonewa, kuma da isa wurin tankar da ke ci da wuta, wutar ta kama tirelar da kuma wasu motoci biyu.”

 

A cikin wani ƙarin bayani, Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ta ce adadin waɗanda suka mutu ya ƙaru daga 48 da aka bayyana da farko zuwa 59 saboda an gano wasu gawarwaki wajen ci gaba da ceto yayin da ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa da ya ƙone sosai ya mutu a Cibiyar Kula da Lafiya ta Tarayya da ke Bida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Za Ta Ci Gaba Da Yin Aiki Tare Da Kasashen Duniya Wajen Sa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mutane Masu Bukata Ta Musamman

Next Post

Sin: Ya Kamata Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Da Afirka Ta Kasance Cikin Adalci, Daidaito Kuma A Bayyane

Related

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

32 minutes ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

4 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

13 hours ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

14 hours ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

16 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

17 hours ago
Next Post
Sin: Ya Kamata Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Da Afirka Ta Kasance Cikin Adalci, Daidaito Kuma A Bayyane

Sin: Ya Kamata Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Da Afirka Ta Kasance Cikin Adalci, Daidaito Kuma A Bayyane

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.