ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fashewar Tankar Mai: Minista Ya Jajanta Wa Al’ummar Neja Da Iyalan Mutum 59 Da Suka Mutu

by Sulaiman
2 years ago
Yajin aiki

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, a ranar Litinin ya jajanta wa al’ummar Jihar Neja bisa rasuwar mutane 59 a wani haɗarin mota da ya ritsa da su a hanyar Bida-Agaie-Lapai ranar Lahadi.

 

A cikin saƙon ta’aziyya da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim, ya sanya wa hannu, ya ce, lamarin ya girgiza Jihar Neja da ƙasa baki ɗaya.

ADVERTISEMENT
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tankar Mai Ta Fashe Ta Kashe Mutane 30 A Neja
  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Kungiyar Kasashen Musulmi A Bangarori Daban-Daban

Ya yi addu’ar Allah ya ba iyalan mamatan ikon jure wannan babban rashin.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Idris ya ce: “Ina miƙa ta’aziyya ta ga gwamnati da al’ummar Jihar Neja da iyalai, abokai da ‘yan’uwan mutane 48 da suka rasa rayukan su a wani mummunan hatsari da ya auku a hanyar Bida-Agaie-Lapai a Jihar Neja da sanyin safiyar Lahadi, 8 ga Satumba, 2024.

 

“Wannan mummunan lamari ya girgiza ɗaukacin Jihar Neja da ma ƙasa baki ɗaya kuma ina yi wa duk waɗanda abin ya shafa a wannan lokaci mai zafi addu’a. Don haka ina taya al’ummar Jihar Neja da ma Nijeriya baki ɗaya alhinin wannan babban rashi.

 

“Allah ya jiƙan waɗanda suka rasu kuma Allah ya bai wa iyalan su juriyar wannan rashi mara misaltuwa.”

 

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC), reshen Jihar Neja, Mista Kumar Tsukwan, ya shaida wa manema labarai a ranar Litinin cewa dukkan waɗanda abin ya shafa maza ne, kuma da ba a iya tantance motocin da abin ya shafa ba saboda tsananin ƙonewar su.

 

Tsukwan ya bayyana cewa lambar mota ɗaya kacal ce aka iya tantancewa, yayin da ba a gane lambobin sauran ba.

Ya ƙara da cewa lamarin ya faru ne da ƙarfe 4:30 na safe kuma an kai rahoton lamarin ga sashin Lapai na FRSC da ƙarfe 4:40 na safe.

 

Ya ce: “Motar tankar man da ke ɗauke da mai daga Legas zuwa Kano tana gudu sosai, inda ta ƙwace ta faɗi ta kama da wuta yayin da wutar ta shafi wata tirela da ke ɗauke da shanu da mutane tare da wasu motoci biyu a baya. Dukkan motocin guda huɗu sun ƙone ƙurmus.”

“An ruwaito cewa sai da ɗaya daga cikin fasinjojin tirelar da ke ɗauke da mutane da shanun ya ankarar da direban cewa akwai wuta fa a gaban su amma sai direban ya amsa da cewa taya ce kawai ke ƙonewa, kuma da isa wurin tankar da ke ci da wuta, wutar ta kama tirelar da kuma wasu motoci biyu.”

 

A cikin wani ƙarin bayani, Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ta ce adadin waɗanda suka mutu ya ƙaru daga 48 da aka bayyana da farko zuwa 59 saboda an gano wasu gawarwaki wajen ci gaba da ceto yayin da ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa da ya ƙone sosai ya mutu a Cibiyar Kula da Lafiya ta Tarayya da ke Bida.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Sin: Ya Kamata Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Da Afirka Ta Kasance Cikin Adalci, Daidaito Kuma A Bayyane

Sin: Ya Kamata Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Da Afirka Ta Kasance Cikin Adalci, Daidaito Kuma A Bayyane

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.