• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya

by Bello Hamza
10 months ago
in Manyan Labarai, Rahotonni
0
Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yanzu da bukatar dashen koda da hanta suke kara karuwa a musamman a kasashe masu tasowa, ana nuna damuwa a kan yadda safarar sassan jikin dan adam ke karuwa a Nijeriya musamama kuma ga wadanda suka dandana dadin safarar sassan jikin mutanen.

Ana samun karuwar wannan muguwar sana’a a kasashe masu tasowa, musamman a tsakanin mutanen da suke samun kazamin kudi ta hanyar abin a Nijeriya kamar yadda sashin bincike musamman na LEADERSHIP ya gano.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Xi Ya Taya Tebboune Murnar Sake Zama Shugaban Algeria

Masana sun ce harkar cire wani sashi a jiki mutum abu ne da ba shi da kyau kuma yana zama wani nau’i na cin zarafin bil adam, inda ake yaudarar mutane da ke da matsalolin rayuwa a cuce su. Ana bukatar wasu mutane marasa imani wajen aiwatar da wannan muguwar sana’a da ke cire wa mutum sassan jikinsa.

Wasu ‘yan Nijeriyan da lamarin yake damu su sun bukaci dukkan masu ruwa da tsaki a bangaren kiwon lafiya su hada karfi da karfe domin samun nasarar fattatakar safarar sassan jikin da adam a kasar nan.

Biciken LEADERSHIP ya kuma nuna cewa, a kwai alaka a kan yadda ake samun karuwar garkuwa da mutane da karuwar haramtattciyar sana’ar ta safarar sassan jikin mutane a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

Misali a shekarar 2023, wani dalibin Jami’ar Fatakwal ya kashe budurwarsa inda ya cire mata wani sashen jikinta da niyyar yin tsafi da shi. An kuma gano cewa, sashen jikin da aka fi safararsa a Nijeriya shi ne koda.

Bayanai daga cibiyar tattara bayanai da karbar gudunmawa da dashen koda ta ‘Global Database on Donation and Transplantation’ sun nuna cewa a tsakanin shekarar 2015 da 2020, an yi dashen koda fiye da 651 ba bisa ka’ida ba a Nijeriya.

An kiyasta cewa, safarar sassan mutum ba bisa ka’ida ba a duniya na samar da tsakanin Dala miliya 840 da dala biliyan 1.7 a duk shekara a fadin duniya. Ana kuma sayen koda a kan ‘yan daloli a kasashe masu tasowa, daga bisani a sayar tsakanin dala 20,000 zuwa 30,000 a kasashen da suka ci gaba. An kuma kiyasta yin dashen koda fiye da 129,681 a shekarar 2020 kawai, inda aka samu koda 36,125 daga wadada suka mutu. Wannan ke nuna ana yin dashen koda akalla 15 a kusan duk awa 1 a duniya.

Saboda tsanannin rayuwa, a yanzu wasu ‘yan Nijeriya da dama suna sayar da wasu sassan jikinsu masu muhimmaci wanda hakan yana sanya rayuwarsu a cikin hadari. Wasu matan Nijeriya na shan wasu kwayoyi domin ya haifar musu da wani yanayi da kwan jikinsu zai bunkasa daga nan sai su sayar da su ga cibiyoyin bincike. Wasu dalibai mata na jami’a suna kuma sayar da kwan haihuwarsu ga masu bukata, masu amfani da shi wajen samar da jarirai ta fasahar ‘IBF’.

Ba kamar yadda abin yake a manyan kasashe ba, mata ke bayar da kwansu a karkashin kulawa da sa idon dokoki, amma a Nijeriya kananan ‘yan mata na sayar da kwansu kusan akalla a kan Naira 50,000.

An kuma samu wasu rahottanin da ke nuna yadda ake tilasta wa ‘yan mata sayar da kwansu a kan dan kudin da bai kai ya kawo ba. Akwai rahottanin kafafen yada labaru da ke nuna cewa, wasu matan masu shekara 16 na sayar da kwansu ba tare da samun jagoranci daga wani wakili ba.

A kwanaki ne, wani magidanci mai suna Olaniyi Iyiol, dan shekara 41 mazaunin Jihar Ondo ya bayyana cewa, talauci ya sa shi yanke shawarar sayar da daya daga cikin kodarsa duk da kuma yana sane da kasadar da ke tattare da dokokin yin haka da kuma yadda abin zai iya shafar lafiyarsa, amma saboda ba shi da wata hanya ta ciyar da iyalansa ya sa ya yanke wannan shawarar.

Wani abin takaii game da wannan lamarin kuma shi ne yadda wasu ‘yan Nijeriya masara imani ke daukar wasu matasa maza da mata daga kauyuka da alkawarin za a samar musu da aikin yi a birane amma cikakken dalin dauko su shi ne a cire musu wasu sassa a jikinsu domin a sayar.

A shekarar da ta gabata, tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ike Ekweremadu da matarsa Beatrice da wani likita mai suna Dr Obinna Obeta, sun shiga hannu, aka kuma daure su a kasar Birtaniya saboda yaudarar wani matashi mai suna Dabid Nwamini, suka kai shi Birtaniya da niyyar cire masa koda domin a ba ‘yar Ekweremadu Sonia Ekweremadu, wadda ke fama da ciwon koda.

An daure Ekweremadu da abokan burninsa ne na tsawon shekaru a gidan yari bisa laifin safarar mutum zuwa kasar Birtaniya.

Wasu masu ruwa da tsaki sun nuna damuwa a kan yadda ake shigar da likitoci a wanan dambarwar.

A Abuja babbar birnin tarayyar kasar nan, an gano masu safarar sassan jikin mutane ba bisa ka’ida ba, bayan da aka gano wasu gungun masu aikata laifi da suka yaudari wani matashi dan shekara 16 mai suna Yahaya Musa, zuwa asibiti a Abuja tare da cire masa koda.

A wani rahoton da aka yada ta tashar talabijin ta intanet ta LEADERSHIP TB a makon da ya wuce, wani mutum mai suna Malam Musa ya bayyana cewa, an yi masa alkawarin naira miliyan 1 in ya yarda ya bayar da kodarasa. Ya yi bayani ne a mastayin mai bayar da shaida a babbar kotun babbar birnin tarayya Abuja da ke Zuba yayin da ake shari’ar ma’akata 4 na asibitin ‘Alliance Hospital and Serbices Ltd’, wadanda ake zargi da cire sassan jikin mutane ba da cikakken izini ba.

Hukumar yaki da safarar mutane ta (NAPTIP) ta gurfanar da Dr. Christopher Otabor, Emmanuel Olorunlaye, Chikaodili Ugochukwu, and Dr. Aremu Abayomi inda take tuhumar su da laifuka 11 da suka hada da cire sassan jikin dan adam ba tare da izinini ba. Babban lauya, Hassan Dahiru, ya bayyana yadda wadannan jami’an asibitin ke kan gaba wajen cire wa mutane sassan jiki.

Wannan wani misali ne na yadda rashin sanin doka da kuma hadarin da ke tattare da harkar cire sassan jiki ke azalzala lamarin safarar sassan jiki, haka kuma halin talauci da natsin rayuwa yana jefa wasu matasan fadawa tarkon masu safarar sassan jiki.

A martaninsa kan yadda lamarin yake kara kamari, shugaban kungiyar likitocin yankin Abuja, Dr Charles Ugwuanyi, ya nemi a samar da dokar da za ta taka wa masu safarar sassan dan adam birki, ya ce lamarin akwai tashin hankali ta yadda ake amfani da halin matsin rayuwua da talauci da al’umma ke ciki wajen jefa su halin da zai iya kai ga rasa rayukansu

Haka kuma wani abbban likita mai suna Oluwole Adeleke, ya ce a halin yanzu ya kamata masu ruwa da tsaki su shigo domin kawo karshen wannan lamarin gaba daya ba tare da bata lokaci ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NijeriyaSafaraSassan JikiTalauci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Kusa Ƙaddamar Da Shirin Yarjejeniyar ÆŠa’a Ta Ƙasa, inji Minista 

Next Post

Siffofin Manzon Allah (SAW)

Related

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

9 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

16 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

20 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

2 days ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

2 days ago
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

2 days ago
Next Post
Siffofin Manzon Allah (SAW)

Siffofin Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.