• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Jagororin ‘Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

by Sulaiman
1 year ago
Sojoji

An tabbatar da kashe wasu Kasurguman jagororin ‘yan bindiga biyu, Sani Black da Kachalla Makore a Zamfara.

 

‘Yan ta’addan biyu na da alhakin kai hare-haren ta’addanci a gundumomin Dansadau da kewaye da kuma wasu sassan karamar hukumar Maru.

  • Gwamnan Anambra Ya Amince Da Biyan Mafi Karancin Albashi Na Naira 70,000
  • Adadin Tashoshin Sadarwa Na 5G Ya Kai Miliyan 4 A Kasar Sin 

Da yake tabbatar da kisan, babban mai bai wa gwamnan jihar Zamfara shawara kan harkokin yada labarai da sadarwa, Alhaji Mustapha Jafaru Kaura, ya ce, an kashe Sani Black ne a ranar Lahadin da ta gabata a kauyen Yar-Tasha yayin da kuma aka kashe Kachalla Makore a ranar Talata a kauyen Kunkeli da ke karamar hukumar Maru a jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Kaura ya bayyana cewa, an kashe fitattun jagororin ‘yan bindigan biyu ne tare da wasu abokan ta’addancinsu su 23 a wani farmakin hadin gwiwa da jami’an hukumar kare hakkin jama’a ta jihar Zamfara (CPG) da sojojin Nijeriya suka kai.

 

“Bayan an kashe Sani Black a wani harin kwantan bauna da aka yi a kauyen Yar’Tasha a ranar Lahadi, 22 ga Satumba, 2024, Kachalla Makore ya tattaro mutanensa a ranar Talata, 24 ga watan Satumba ya nufi Yar-Tasha domin kwato gawar Black da kuma daukar fansa.

 

“An yi nasara shi ma an yi masa kwanton bauna kuma aka kashe shi a kauyen Kunkeli da ke gundumar Dansadau a karamar hukumar Maru.

 

“An kashe Sani Black ne tare da mutanensa guda takwas yayin da aka kashe Makore tare da mutanensa 15.

 

“Makore ya kona motar sulke ta sojoji tare da raunata wasu sojoji biyu a lokacin arangamar da jami’an tsaron a kauyen Kunkeli,” inji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Next Post
“Labarina Game Da Kasar Sin”

“Labarina Game Da Kasar Sin”

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.