• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asirin Amurka A Fannin Tada “Yakin Hakkin Dan Adam” A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Asirin Amurka A Fannin Tada “Yakin Hakkin Dan Adam” A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zuwa yau 9 ga watan Oktoba aka cika wata daya da gudanar da taro na 57 na kwamitin kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, inda kasashe sama da 100 suka bayyana goyon bayansu ga kasar Sin ta hanyoyin gabatar da jawabi tare ko daya bayan daya, wajen jaddada cewa, harkokin Xinjiang, da Hong Kong, da Xizang(Tibet), harkokin cikin gida ne na kasar Sin, kuma bai kamata Amurka ta yi shisshigi a ciki ba. Al’amarin da ya shaida cewa, yunkurin Amurka da sauran wasu kasashe ‘yan kalilan na yammacin duniya na siyasantar da batun hakkin dan Adam, ba zai samu nasara ba.

 

Amurka ta kawar da ido daga matsalolin da ita kanta take fuskanta ta fannin kare hakkin Adam, kuma tana fakewa da batun hakkin dan Adam wajen matsawa sauran kasashe lamba, gami da nuna fin karfi a duniya.

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Mara Baya Ga Kasashen Yankin Manyan Tafkunan Afirka Don Karfafa Hadin Gwiwa
  • Xi Jinping Ya Karfafawa Kungiyar Red Cross Ta Sin Gwiwar Karfafa Ayyukan Jin Kai

Domin tsoma baki cikin harkokin cikin gidan sauran kasashe, abu na farko da Amurka ta kan yi, shi ne kirkiro “laifin da ya shafi hakkin dan Adam”. Bari mu dauki kasar Venezuela a matsayin misali. A ’yan shekarun nan, bisa hujjar wai Venezuela ta aikata laifi a fannin kare hakkin dan Adam, Amurka ta fadada kakaba mata takunkumin tattalin arziki, al’amarin da ya haifar wa Venezuela matsalolin tattalin arziki da jin kai da kuma ci gaba.

 

Labarai Masu Nasaba

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Baya ga gwamnati da kafafen yada labarai, wani muhimmin abu da ya taka muhimmiyar rawa a cikin “yakin hakkin dan Adam” da Amurka ta tayar a sauran kasashe, shi ne NGO, wato kungiyoyin da ba na gwamnati ba. Wasu kungiyoyin da ba na gwamnati ba a Amurka, wadanda suka fake da sunan kare “demokuradiyya” da “hakkin dan Adam”, sun yi yunkurin rura wutar rikicin kawo baraka, da kulla makiricin tada rikicin siyasa, da shirga karya da sauransu a sassan kasa da kasa.

 

A Majalisar Dinkin Duniya kuwa, Amurka ta kan bada shawarar zartas da kudurorin kasa iri-iri ta hanyar fakewa da batun hakkin Adam, inda ta kan nuna yatsa ga wasu kasashe masu tasowa, da matsa musu lamba a fannin siyasa, kana ta kan yi yunkurin kawo cikas ga wasu batutuwan gaggawa da suka shafi jin kai.

 

Akasarin kasashe masu tsayawa kan adalci da gaskiya sun riga sun fahimci wayon Amurka, wato yunkurin da take na yin shisshigi cikin harkokin cikin gidan kasar Sin da na sauran kasashe masu tasowa, ta hanyar amfani da batun hakkin dan Adam. Muryoyin kasashe sama da 100 sun shaida cewa, yunkurin da Amurka da sauran wasu kasashe ’yan kalilan suka yi, ba zai yi nasara ba. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Dawo Da Tsohon Farashin Man Fetur Cikin Gaggawa – NLC

Next Post

Dorewar Bunkasuwar Tattalin Arzikin Sin Ta Karawa Duniya Kwarin Gwiwa

Related

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

1 hour ago
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya
Daga Birnin Sin

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

2 hours ago
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO
Daga Birnin Sin

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

3 hours ago
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire
Daga Birnin Sin

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

4 hours ago
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

5 hours ago
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha
Daga Birnin Sin

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

6 hours ago
Next Post
Dorewar Bunkasuwar Tattalin Arzikin Sin Ta Karawa Duniya Kwarin Gwiwa

Dorewar Bunkasuwar Tattalin Arzikin Sin Ta Karawa Duniya Kwarin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.