ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asirin Amurka A Fannin Tada “Yakin Hakkin Dan Adam” A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Amurka

Zuwa yau 9 ga watan Oktoba aka cika wata daya da gudanar da taro na 57 na kwamitin kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, inda kasashe sama da 100 suka bayyana goyon bayansu ga kasar Sin ta hanyoyin gabatar da jawabi tare ko daya bayan daya, wajen jaddada cewa, harkokin Xinjiang, da Hong Kong, da Xizang(Tibet), harkokin cikin gida ne na kasar Sin, kuma bai kamata Amurka ta yi shisshigi a ciki ba. Al’amarin da ya shaida cewa, yunkurin Amurka da sauran wasu kasashe ‘yan kalilan na yammacin duniya na siyasantar da batun hakkin dan Adam, ba zai samu nasara ba.

 

Amurka ta kawar da ido daga matsalolin da ita kanta take fuskanta ta fannin kare hakkin Adam, kuma tana fakewa da batun hakkin dan Adam wajen matsawa sauran kasashe lamba, gami da nuna fin karfi a duniya.

ADVERTISEMENT
  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Mara Baya Ga Kasashen Yankin Manyan Tafkunan Afirka Don Karfafa Hadin Gwiwa
  • Xi Jinping Ya Karfafawa Kungiyar Red Cross Ta Sin Gwiwar Karfafa Ayyukan Jin Kai

Domin tsoma baki cikin harkokin cikin gidan sauran kasashe, abu na farko da Amurka ta kan yi, shi ne kirkiro “laifin da ya shafi hakkin dan Adam”. Bari mu dauki kasar Venezuela a matsayin misali. A ’yan shekarun nan, bisa hujjar wai Venezuela ta aikata laifi a fannin kare hakkin dan Adam, Amurka ta fadada kakaba mata takunkumin tattalin arziki, al’amarin da ya haifar wa Venezuela matsalolin tattalin arziki da jin kai da kuma ci gaba.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Baya ga gwamnati da kafafen yada labarai, wani muhimmin abu da ya taka muhimmiyar rawa a cikin “yakin hakkin dan Adam” da Amurka ta tayar a sauran kasashe, shi ne NGO, wato kungiyoyin da ba na gwamnati ba. Wasu kungiyoyin da ba na gwamnati ba a Amurka, wadanda suka fake da sunan kare “demokuradiyya” da “hakkin dan Adam”, sun yi yunkurin rura wutar rikicin kawo baraka, da kulla makiricin tada rikicin siyasa, da shirga karya da sauransu a sassan kasa da kasa.

 

A Majalisar Dinkin Duniya kuwa, Amurka ta kan bada shawarar zartas da kudurorin kasa iri-iri ta hanyar fakewa da batun hakkin Adam, inda ta kan nuna yatsa ga wasu kasashe masu tasowa, da matsa musu lamba a fannin siyasa, kana ta kan yi yunkurin kawo cikas ga wasu batutuwan gaggawa da suka shafi jin kai.

 

Akasarin kasashe masu tsayawa kan adalci da gaskiya sun riga sun fahimci wayon Amurka, wato yunkurin da take na yin shisshigi cikin harkokin cikin gidan kasar Sin da na sauran kasashe masu tasowa, ta hanyar amfani da batun hakkin dan Adam. Muryoyin kasashe sama da 100 sun shaida cewa, yunkurin da Amurka da sauran wasu kasashe ’yan kalilan suka yi, ba zai yi nasara ba. (Murtala Zhang)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina Kasa

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Dorewar Bunkasuwar Tattalin Arzikin Sin Ta Karawa Duniya Kwarin Gwiwa

Dorewar Bunkasuwar Tattalin Arzikin Sin Ta Karawa Duniya Kwarin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Amurka

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Amurka

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.