• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai bibiyar ci gaban da kasar Sin ta samu musamman a gwamman shekarun da suka gabata, tilas ya amince cewa salon da kasar ke bi wajen zamanantar da kai ya ciri tuta, duba da yadda ya haifarwa ’yan kasar da mai ido ta fuskar tsame alumma daga kangin talauci, da samarwa alummar Sinawa damar more ababen more rayuwa masu inganci, da raya fasahohin zamani da sauransu, wadanda dukkanin su ke zama muhimmin misali mai kima ga sauran kasashe masu tasowa musamman na Afirka.

 

Kasashen Afirka na iya koyi da dabarun kasar Sin ta fuskar aiwatar da managartan manufofin raya kai, da gudanar da sauye-sauye da zamanantarwa, ta yadda su ma za su daga matsayin su daga kasashen da alummun suke fama da karancin karfin tattalin arziki zuwa cibiyoyin raya tattalin arziki a matakin kasa da kasa.

  • Xi Ya Mika Gaisuwar Ban Girma Ga Dattawa A Jajibirin Ranar Tsofaffin Kasar Sin
  • Ban Yi Nadamar Yakar PDP A Zaben 2023 Ba – Wike

Mun dai ga misalan hakan a bangaren kasar Sin, wadda ta kawar da fatara, da cike gibi tsakanin mawadata da masu rauni, zuwa wanzar da ci gaba mai dorewa a dukkanin fannoni, matakan da suka kai kasar zuwa turbar samun ci gaba a dukkanin bangarori, da daidaita tafiya tsakanin raya tattalin arzikin kasa da ci gaban zamantakewa da walwalar alumma.

 

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

A daya hannun, muna iya cewa yadda kasashen Afirka ke kara rungumar tafiyar samar da ci gaba tare da kasar Sin, karkashin tsare-tsare, da dandaloli daban daban abun a yaba ne. A duk inda muka duba muna iya ganin ayyukan hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka na raba ababen more rayuwa, da musayar kwarewa, da musayar aladu, da karfafa kawance, da bunkasa cinikayyar hajoji da hidimomi tsakanin sassan biyu.

 

Baya ga hakan, wasu karin sassa da ya kamata sassan biyu su inganta hadin gwiwa su ne batun samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da kare muhallin halittu, da rage tasirin dumamar yanayi, da raya samar da makamashi mai tsafta, fannonin da tuni kasar Sin ta yi nisa a fannin cimma nasarar su.

 

Yayin da ake duba yiwuwar fadada kawance, da cudanya tsakanin Sin da kasashen Afirka a dukkanin fannoni, wajibi ne a jinjinawa yadda Sin din ke fadada tallafin da take baiwa kasashen Afirka ta fuskoki da dama, kamar samar da yankunan raya masanaantu, da yankunan cinikayya maras shinge, da taimakon raya fasahohin noma na zamani da dai sauran su.

 

Kaza lika, ya zama dole a yabawa kasar Sin don gane da sabbin shirye-shiryen hadin gwiwa 10 da ta gabatar a baya bayan nan, don ingiza zamanantar da kasashen Afirka abokan tafiyarta, shirye-shiryen da ko shakka babu za su yaukaka dunkulewar ayyukan hadin kan sassan biyu, kana sun dace da ajandar raya nahiyar Afirka ta nan zuwa shekarar 2063, da ma ajandar raya yankin cinikayya maras shinge na daukacin kasahen Afirka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mijina Ba Ne Sanadin Ƙuncin Rayuwa Da Ake Ciki A Nijeriya – Uwargidan Shugaban Ƙasa

Next Post

Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

18 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

19 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

20 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

21 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

22 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

2 days ago
Next Post
Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

LABARAI MASU NASABA

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.